Surah Ar-Rahman (undefined) is the 55th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Medina and contains 78 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 55:1
ٱلرَّحْمَٰنُ
Ar Rahmaan
(Allah) Mai rahama.
- 55:2
عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ
'Allamal Quran
Yã sanar da Alƙur'ani.
- 55:3
خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ
Khalaqal insaan
Yã halitta mutum.
- 55:4
عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ
'Allamalhul bayaan
Yã sanar da shi bayãni (magana).
- 55:5
ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍۢ
Ashshamsu walqamaru bihusbaan
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
- 55:6
وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
Wannajmu washshajaru yasjudan
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
- 55:7
وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ
Wassamaaa'a rafa'ahaa wa wada'al Meezan
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
- 55:8
أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ
Allaa tatghaw fil meezaan
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
- 55:9
وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ
Wa aqeemul wazna bilqisti wa laa tukhsirul meezaan
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
- 55:10
وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
Wal arda wada'ahaa lilanaame
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
- 55:11
فِيهَا فَٰكِهَةٌۭ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ
Feehaa faakihatunw wan nakhlu zaatul akmaam
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
- 55:12
وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ
Walhabbu zul 'asfi war Raihaanu
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
- 55:13
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
- 55:14
خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ مِن صَلْصَٰلٍۢ كَٱلْفَخَّارِ
Khalaqal insaana min salsaalin kalfakhkhaari
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
- 55:15
وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍۢ مِّن نَّارٍۢ
Wa khalaqal jaaan mim maarijim min naar
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
- 55:16
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:17
رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ
Rabbul mashriqayni wa Rabbul maghribayni
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
- 55:18
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:19
مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
Marajal bahrayni yalta qiyaani
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
- 55:20
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ
Bainahumaa barzakhul laa yabghiyaan
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
- 55:21
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:22
يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ
Yakhruju minhumal lu 'lu u wal marjaanu
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
- 55:23
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:24
وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَٰمِ
Wa lahul jawaaril mun sha'aatu fil bahri kal a'laam
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
- 55:25
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:26
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍۢ
Kullu man 'alaihaa faan
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
- 55:27
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
Wa yabqaa wajhu rabbika zul jalaali wal ikraam
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
- 55:28
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:29
يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍۢ
Yas'aluhoo man fissamaawaati walard; kulla ywmin huwa fee shaan
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
- 55:30
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:31
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ
Sanafrughu lakum ayyuhas saqalaan
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!
- 55:32
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:33
يَٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَٰنٍۢ
Yaa ma'sharal jinni wal insi inis tata'tum an tanfuzoo min aqtaaris samaawaati wal ardi fanfuzoo; laa tanfuzoona illaa bisultaan
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
- 55:34
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:35
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌۭ مِّن نَّارٍۢ وَنُحَاسٌۭ فَلَا تَنتَصِرَانِ
Yursalu 'alaikumaa shuwaazum min naarifiw-wa nuhaasun falaa tantasiraan
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?
- 55:36
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:37
فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةًۭ كَٱلدِّهَانِ
Fa-izan shaqqatis samaaa'u fakaanat wardatan kaddihaan
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
- 55:38
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:39
فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌۭ وَلَا جَآنٌّۭ
Fa-yawma'izil laa yus'alu 'an zambiheee insunw wa laa jaann
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
- 55:40
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:41
يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ
Yu'raful mujrimoona biseemaahum fa'yu'khazu binna waasi wal aqdaam
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.
- 55:42
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:43
هَٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ
Haazihee jahannamul latee yukazzibu bihal mujrimoon
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
- 55:44
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍۢ
Yatoofoona bainahaa wa baina hameemim aan
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
- 55:45
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:46
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ
Wa liman khaafa maqaama rabbihee jannataan
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
- 55:47
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:48
ذَوَاتَآ أَفْنَانٍۢ
Zawaataaa afnaan
Mãsu rassan itãce.
- 55:49
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:50
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
Feehimaa 'aynaani tajriyaan
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
- 55:51
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:52
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَٰكِهَةٍۢ زَوْجَانِ
Feehimaa min kulli faakihatin zawjaan
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.
- 55:53
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:54
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍۢ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍۢ
Muttaki'eena 'alaa furushim bataaa'inuhaa min istabraq; wajanal jannataini daan
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.
- 55:55
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:56
فِيهِنَّ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ
Feehinna qaasiratut tarfi lam yatmishunna insun qablahum wa laa jaaann
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.
- 55:57
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:58
كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ
ka annahunnal yaaqootu wal marjaan
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.
- 55:59
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:60
هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَٰنُ
Hal jazaaa'ul ihsaani illal ihsaan
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.
- 55:61
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:62
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
Wa min doonihimaa jannataan
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.
- 55:63
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:64
مُدْهَآمَّتَانِ
Mudhaaammataan
Mãsu duhun inuwa.
- 55:65
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:66
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
Feehimaa 'aynaani nad daakhataan
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.
- 55:67
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:68
فِيهِمَا فَٰكِهَةٌۭ وَنَخْلٌۭ وَرُمَّانٌۭ
Feehimaa faakihatunw wa nakhlunw wa rummaan
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.
- 55:69
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:70
فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌۭ
Feehinna khairaatun hisaan
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.
- 55:71
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:72
حُورٌۭ مَّقْصُورَٰتٌۭ فِى ٱلْخِيَامِ
Hoorum maqsooraatun fil khiyaam
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.
- 55:73
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:74
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ
Lam yatmis hunna insun qablahum wa laa jaaann
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.
- 55:75
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:76
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍۢ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍۢ
Muttaki'eena 'alaa rafratin khudrinw wa 'abqariyyin hisaan
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.
- 55:77
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
- 55:78
تَبَٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
Tabaarakasmu Rabbika Zil-Jalaali wal-Ikraam
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.
About Surah Ar-Rahman
Ar-Rahman, the Most Merciful, is one of the most beautiful surahs in the Quran, with its refrain repeated thirty-one times: so which of the favors of your Lord will you deny. It lists gift after gift, from the sun and moon to the seas, the fruits, and the gardens of Paradise. It is a hymn of gratitude to the Most Merciful.
Themes: The favors of Allah, Gratitude, Creation and balance, Paradise
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.