All Surahs

Surah Al-Qamar (undefined)

سُورَةُ القَمَرِ

Surah 54 of the Holy Quran · Meccan · 55 verses

Also spelled: Qamar, Al Qamar, AlQamar, The Moon

Surah Al-Qamar (undefined) is the 54th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 55 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 54:1

    ٱقْتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلْقَمَرُ

    Iqtarabatis Saa'atu wsan shaqqal qamar

    Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.

  2. 54:2

    وَإِن يَرَوْا۟ ءَايَةًۭ يُعْرِضُوا۟ وَيَقُولُوا۟ سِحْرٌۭ مُّسْتَمِرٌّۭ

    Wa iny yaraw aayatany yu'ridoo wa yaqooloo sihrum mustamirr

    Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"

  3. 54:3

    وَكَذَّبُوا۟ وَٱتَّبَعُوٓا۟ أَهْوَآءَهُمْ ۚ وَكُلُّ أَمْرٍۢ مُّسْتَقِرٌّۭ

    Wa kazzaboo wattaba'ooo ahwaaa'ahum; wa kullu amrim mustaqirr

    Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.

  4. 54:4

    وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّنَ ٱلْأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ

    Wa laqad jaaa'ahum minal ambaaa'i maa feehi muzdajar

    Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.

  5. 54:5

    حِكْمَةٌۢ بَٰلِغَةٌۭ ۖ فَمَا تُغْنِ ٱلنُّذُرُ

    Hikmatum baalighatun famaa tughnin nuzur

    Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.

  6. 54:6

    فَتَوَلَّ عَنْهُمْ ۘ يَوْمَ يَدْعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَىْءٍۢ نُّكُرٍ

    Fatawalla 'anhum; yawma yad'ud daa'i ilaa shai 'in nukur

    Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.

  7. 54:7

    خُشَّعًا أَبْصَٰرُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌۭ مُّنتَشِرٌۭ

    khushsha'an absaaruhum yakrujoona minal ajdaasi ka annahum jaraadum muntashir

    ¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.

  8. 54:8

    مُّهْطِعِينَ إِلَى ٱلدَّاعِ ۖ يَقُولُ ٱلْكَٰفِرُونَ هَٰذَا يَوْمٌ عَسِرٌۭ

    Muhti'eena ilad daa'i yaqoolul kafiroona haazaa yawmun 'asir

    Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"

  9. 54:9

    ۞ كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍۢ فَكَذَّبُوا۟ عَبْدَنَا وَقَالُوا۟ مَجْنُونٌۭ وَٱزْدُجِرَ

    Kazzabat qablahum qawmu Noohin fakazzaboo 'abdanaa wa qaaloo majnoo nunw wazdujir

    Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.

  10. 54:10

    فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّى مَغْلُوبٌۭ فَٱنتَصِرْ

    Fada'aa Rabbahooo annee maghloobun fantasir

    Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."

  11. 54:11

    فَفَتَحْنَآ أَبْوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٍۢ مُّنْهَمِرٍۢ

    Fafatahnaaa abwaabas sa maaa'i bimaa'im munhamir

    Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.

  12. 54:12

    وَفَجَّرْنَا ٱلْأَرْضَ عُيُونًۭا فَٱلْتَقَى ٱلْمَآءُ عَلَىٰٓ أَمْرٍۢ قَدْ قُدِرَ

    Wa fajjamal arda 'uyoonan faltaqal maaa'u 'alaaa amrin qad qudir

    Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.

  13. 54:13

    وَحَمَلْنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلْوَٰحٍۢ وَدُسُرٍۢ

    Wa hamalnaahu 'alaa zaati alwaahinw wa dusur

    Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.

  14. 54:14

    تَجْرِى بِأَعْيُنِنَا جَزَآءًۭ لِّمَن كَانَ كُفِرَ

    Tajree bi a'yuninaa jazaaa 'al liman kaana kufir

    Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.

  15. 54:15

    وَلَقَد تَّرَكْنَٰهَآ ءَايَةًۭ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

    Wa laqat taraknaahaad aayatan fahal mim muddakir

    Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni

  16. 54:16

    فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

    Fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

    To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?

  17. 54:17

    وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

    Wa laqad yassamal Quraana liz zikri fahal mimmuddakir

    Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

  18. 54:18

    كَذَّبَتْ عَادٌۭ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

    Kazzabat 'Aadun fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

    Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?

  19. 54:19

    إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًۭا صَرْصَرًۭا فِى يَوْمِ نَحْسٍۢ مُّسْتَمِرٍّۢ

    Innaa arsalnaa 'alaihim reehan sarsaran fee Yawmi nahsim mustamirr

    Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.

  20. 54:20

    تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍۢ مُّنقَعِرٍۢ

    Tanzi;un naasa ka anna huma'jaazu nakhlim munqa'ir

    Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.

  21. 54:21

    فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

    'Fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

    To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?

  22. 54:22

    وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

    Wa laqad yassamal Quraana liz zikri fahal mim muddakir

    Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

  23. 54:23

    كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ

    Kazzabat Samoodu binnuzur

    Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.

  24. 54:24

    فَقَالُوٓا۟ أَبَشَرًۭا مِّنَّا وَٰحِدًۭا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذًۭا لَّفِى ضَلَٰلٍۢ وَسُعُرٍ

    Faqaalooo a-basharam minnaa waahidan nattabi'uhooo innaa izal lafee dalaalinw wa su'ur

    Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.

  25. 54:25

    أَءُلْقِىَ ٱلذِّكْرُ عَلَيْهِ مِنۢ بَيْنِنَا بَلْ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٌۭ

    'A-ulqiyaz zikru 'alaihi mim baininaa bal huwa kazzaabun ashir

    "Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"

  26. 54:26

    سَيَعْلَمُونَ غَدًۭا مَّنِ ٱلْكَذَّابُ ٱلْأَشِرُ

    Sa-ya'lamoona ghadam manil kazzaabul ashir

    Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?

  27. 54:27

    إِنَّا مُرْسِلُوا۟ ٱلنَّاقَةِ فِتْنَةًۭ لَّهُمْ فَٱرْتَقِبْهُمْ وَٱصْطَبِرْ

    Innaa mursilun naaqati fitnatal lahum fartaqibhum wastabir

    Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.

  28. 54:28

    وَنَبِّئْهُمْ أَنَّ ٱلْمَآءَ قِسْمَةٌۢ بَيْنَهُمْ ۖ كُلُّ شِرْبٍۢ مُّحْتَضَرٌۭ

    Wa nabbi'hum annal maaa'a qismatum bainahum kullu shirbim muhtadar

    Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.

  29. 54:29

    فَنَادَوْا۟ صَاحِبَهُمْ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ

    Fanaadaw saahibahum fata'aataa fa'aqar

    Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,

  30. 54:30

    فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

    Fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

    To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?

  31. 54:31

    إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ صَيْحَةًۭ وَٰحِدَةًۭ فَكَانُوا۟ كَهَشِيمِ ٱلْمُحْتَظِرِ

    Innaaa arsalnaa 'alaihim saihatanw waahidatan fakaano kahasheemil muhtazir

    Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.

  32. 54:32

    وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

    Wa laqad yassarnal quraana liz zikri fahal mim muddakir

    Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

  33. 54:33

    كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍۭ بِٱلنُّذُرِ

    Kazzabat qawmu lootim binnuzur

    Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.

  34. 54:34

    إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٍۢ ۖ نَّجَّيْنَٰهُم بِسَحَرٍۢ

    Innaa arsalnaa 'alaihim haasiban illaaa aala Loot najjainaahum bisahar

    Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.

  35. 54:35

    نِّعْمَةًۭ مِّنْ عِندِنَا ۚ كَذَٰلِكَ نَجْزِى مَن شَكَرَ

    Ni'matam min 'indinaa; kazaalika najzee man shakar

    Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.

  36. 54:36

    وَلَقَدْ أَنذَرَهُم بَطْشَتَنَا فَتَمَارَوْا۟ بِٱلنُّذُرِ

    Wa laqad anzarahum batshatanaa fatamaaraw binnuzur

    Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.

  37. 54:37

    وَلَقَدْ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيْفِهِۦ فَطَمَسْنَآ أَعْيُنَهُمْ فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ

    Wa laqad raawadoohu 'andaifee fatamasnaaa a'yunahum fazooqoo 'azaabee wa nuzur

    Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."

  38. 54:38

    وَلَقَدْ صَبَّحَهُم بُكْرَةً عَذَابٌۭ مُّسْتَقِرٌّۭ

    Wa laqad sabbahahum bukratan 'azaabum mustaqirr

    Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.

  39. 54:39

    فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ

    Fazooqoo 'azaabee wa nuzur

    To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.

  40. 54:40

    وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

    Wa laqad yassarnal Quraana liz zikri fahal mim muddakir

    Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

  41. 54:41

    وَلَقَدْ جَآءَ ءَالَ فِرْعَوْنَ ٱلنُّذُرُ

    Wa laqad jaaa'a Aala Fir'awnan nuzur

    Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.

  42. 54:42

    كَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذْنَٰهُمْ أَخْذَ عَزِيزٍۢ مُّقْتَدِرٍ

    Kazzaboo bi Aayaatinaa kullihaa fa akhaznaahum akhza 'azeezim muqtadir

    Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.

  43. 54:43

    أَكُفَّارُكُمْ خَيْرٌۭ مِّنْ أُو۟لَٰٓئِكُمْ أَمْ لَكُم بَرَآءَةٌۭ فِى ٱلزُّبُرِ

    Akuffaarukum khairum min ulaaa'ikum am lakum baraaa'atun fiz Zubur

    Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?

  44. 54:44

    أَمْ يَقُولُونَ نَحْنُ جَمِيعٌۭ مُّنتَصِرٌۭ

    Am yaqooloona nahnu jamee'um muntasir

    Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"

  45. 54:45

    سَيُهْزَمُ ٱلْجَمْعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ

    Sa yuhzamul jam'u wa yuwalloonad dubur

    Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.

  46. 54:46

    بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوْعِدُهُمْ وَٱلسَّاعَةُ أَدْهَىٰ وَأَمَرُّ

    Balis Saa'atu maw'iduhum was Saa'atu adhaa wa amarr

    Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.

  47. 54:47

    إِنَّ ٱلْمُجْرِمِينَ فِى ضَلَٰلٍۢ وَسُعُرٍۢ

    Innal mujrimeena fee dalaalinw wa su'ur

    Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.

  48. 54:48

    يَوْمَ يُسْحَبُونَ فِى ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمْ ذُوقُوا۟ مَسَّ سَقَرَ

    Yawma yushaboona fin Naari'alaa wujoohimim zooqoo massa saqar

    Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."

  49. 54:49

    إِنَّا كُلَّ شَىْءٍ خَلَقْنَٰهُ بِقَدَرٍۢ

    Innaa kulla shai'in khalaqnaahu biqadar

    Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.

  50. 54:50

    وَمَآ أَمْرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٌۭ كَلَمْحٍۭ بِٱلْبَصَرِ

    Wa maaa amrunaaa illaa waahidatun kalamhim bilbasar

    Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.

  51. 54:51

    وَلَقَدْ أَهْلَكْنَآ أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

    Wa laqad ahlaknaaa ashyaa'akum fahal mim muddakir

    Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?

  52. 54:52

    وَكُلُّ شَىْءٍۢ فَعَلُوهُ فِى ٱلزُّبُرِ

    Wa kullu shai'in fa'aloohu fiz Zubur

    Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.

  53. 54:53

    وَكُلُّ صَغِيرٍۢ وَكَبِيرٍۢ مُّسْتَطَرٌ

    Wa kullu sagheerinw wa kabeerim mustatar

    Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.

  54. 54:54

    إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍۢ وَنَهَرٍۢ

    Innal muttaqeena fee jannaatinw wa nahar

    Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.

  55. 54:55

    فِى مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍۢ مُّقْتَدِرٍۭ

    Fee maq'adi sidqin 'inda Maleekim Muqtadir

    A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.

About Surah Al-Qamar

Al-Qamar, the Moon, opens with the splitting of the moon as a sign and repeats a striking refrain: that Allah has made the Quran easy to remember, so is there anyone who will take heed. It recalls the nations of Nuh, 'Ad, Thamud, Lut, and Pharaoh, each warned and each accountable. The rhythm makes it memorable and sobering.

Themes: The splitting of the moon, The Quran made easy, Past nations, Taking heed

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.