All Surahs

Surah Al-Waqi'ah (undefined)

سُورَةُ الوَاقِعَةِ

Surah 56 of the Holy Quran · Meccan · 96 verses

Also spelled: Waqi'ah, Al Waqi'ah, AlWaqi'ah, The Inevitable, Al-Waqia, Waqiah, The Event

Surah Al-Waqi'ah (undefined) is the 56th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 96 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 56:1

    إِذَا وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ

    Izaa waqa'atil waaqi'ah

    Idan mai aukuwa ta auku.

  2. 56:2

    لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ

    Laisa liwaq'atihaa kaazibah

    Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.

  3. 56:3

    خَافِضَةٌۭ رَّافِعَةٌ

    Khafidatur raafi'ah

    (Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.

  4. 56:4

    إِذَا رُجَّتِ ٱلْأَرْضُ رَجًّۭا

    Izaa rujjatil ardu rajjaa

    Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.

  5. 56:5

    وَبُسَّتِ ٱلْجِبَالُ بَسًّۭا

    Wa bussatil jibaalu bassaa

    Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.

  6. 56:6

    فَكَانَتْ هَبَآءًۭ مُّنۢبَثًّۭا

    Fakaanat habaaa'am mumbassaa

    Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.

  7. 56:7

    وَكُنتُمْ أَزْوَٰجًۭا ثَلَٰثَةًۭ

    Wa kuntum azwaajan salaasah

    Kuma kun kasance nau'i uku.

  8. 56:8

    فَأَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ

    Fa as haabul maimanati maaa as haabul maimanah

    Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

  9. 56:9

    وَأَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ

    Wa as haabul mash'amati maaa as haabul mash'amah

    Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?

  10. 56:10

    وَٱلسَّٰبِقُونَ ٱلسَّٰبِقُونَ

    Wassaabiqoonas saabiqoon

    Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,

  11. 56:11

    أُو۟لَٰٓئِكَ ٱلْمُقَرَّبُونَ

    Ulaaa'ikal muqarraboon

    Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.

  12. 56:12

    فِى جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

    Fee Jannaatin Na'eem

    A ckin Aljannar ni'ima.

  13. 56:13

    ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

    Sullatum minal awwaleen

    Jama'a ne daga mutãnen farko.

  14. 56:14

    وَقَلِيلٌۭ مِّنَ ٱلْءَاخِرِينَ

    Wa qaleelum minal aa khireen

    Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.

  15. 56:15

    عَلَىٰ سُرُرٍۢ مَّوْضُونَةٍۢ

    'Alaa sururim mawdoonah

    (Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.

  16. 56:16

    مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيْهَا مُتَقَٰبِلِينَ

    Muttaki'eena 'alaihaa mutaqabileen

    Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.

  17. 56:17

    يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَٰنٌۭ مُّخَلَّدُونَ

    Yatoofu 'alaihim wildaa num mukkhalladoon

    Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.

  18. 56:18

    بِأَكْوَابٍۢ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍۢ مِّن مَّعِينٍۢ

    Bi akwaabinw wa abaareeq, wa kaasim mim ma'een

    Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.

  19. 56:19

    لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ

    Laa yusadda'oona 'anhaa wa laa yunzifoon

    Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.

  20. 56:20

    وَفَٰكِهَةٍۢ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ

    Wa faakihatim mimmaa yatakhaiyaroon

    Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.

  21. 56:21

    وَلَحْمِ طَيْرٍۢ مِّمَّا يَشْتَهُونَ

    Wa lahmi tairim mimmaa yashtahoon

    Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.

  22. 56:22

    وَحُورٌ عِينٌۭ

    Wa hoorun'een

    Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.

  23. 56:23

    كَأَمْثَٰلِ ٱللُّؤْلُؤِ ٱلْمَكْنُونِ

    Ka amsaalil lu'lu'il maknoon

    Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.

  24. 56:24

    جَزَآءًۢ بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ

    Jazaaa'am bimaa kaanoo ya'maloon

    A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.

  25. 56:25

    لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا تَأْثِيمًا

    Laa yasma'oona feehaa laghwanw wa laa taaseemaa

    Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.

  26. 56:26

    إِلَّا قِيلًۭا سَلَٰمًۭا سَلَٰمًۭا

    Illaa qeelan salaaman salaamaa

    Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.

  27. 56:27

    وَأَصْحَٰبُ ٱلْيَمِينِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْيَمِينِ

    Wa as haabul yameeni maaa as haabul Yameen

    Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

  28. 56:28

    فِى سِدْرٍۢ مَّخْضُودٍۢ

    Fee sidrim makhdood

    (Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.

  29. 56:29

    وَطَلْحٍۢ مَّنضُودٍۢ

    Wa talhim mandood

    Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.

  30. 56:30

    وَظِلٍّۢ مَّمْدُودٍۢ

    Wa zillim mamdood

    Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.

  31. 56:31

    وَمَآءٍۢ مَّسْكُوبٍۢ

    Wa maaa'im maskoob

    Da wani ruwa mai gudãna.

  32. 56:32

    وَفَٰكِهَةٍۢ كَثِيرَةٍۢ

    Wa faakihatin kaseerah

    Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.

  33. 56:33

    لَّا مَقْطُوعَةٍۢ وَلَا مَمْنُوعَةٍۢ

    Laa maqtoo'atinw wa laa mamnoo'ah

    Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.

  34. 56:34

    وَفُرُشٍۢ مَّرْفُوعَةٍ

    Wa furushim marfoo'ah

    Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.

  35. 56:35

    إِنَّآ أَنشَأْنَٰهُنَّ إِنشَآءًۭ

    Innaaa anshaanaahunna inshaaa'aa

    Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.

  36. 56:36

    فَجَعَلْنَٰهُنَّ أَبْكَارًا

    Faja'alnaahunna abkaaraa

    Sa'an nan Muka sanya su budurwai.

  37. 56:37

    عُرُبًا أَتْرَابًۭا

    'Uruban atraabaa

    Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.

  38. 56:38

    لِّأَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ

    Li as haabil yameen

    Ga mazõwa dãma.

  39. 56:39

    ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

    Sullatum minal awwa leen

    Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

  40. 56:40

    وَثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْءَاخِرِينَ

    Wa sullatum minal aakhireen

    Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

  41. 56:41

    وَأَصْحَٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلشِّمَالِ

    Wa as haabush shimaali maaa as haabush shimaal

    Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

  42. 56:42

    فِى سَمُومٍۢ وَحَمِيمٍۢ

    Fee samoominw wa hameem

    Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

  43. 56:43

    وَظِلٍّۢ مِّن يَحْمُومٍۢ

    Wa zillim miny yahmoom

    Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

  44. 56:44

    لَّا بَارِدٍۢ وَلَا كَرِيمٍ

    Laa baaridinw wa laa kareem

    Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

  45. 56:45

    إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ

    Innaahum kaanoo qabla zaalika mutrafeen

    Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

  46. 56:46

    وَكَانُوا۟ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلْحِنثِ ٱلْعَظِيمِ

    Wa kaanoo yusirroona 'alal hinsil 'azeem

    Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

  47. 56:47

    وَكَانُوا۟ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ

    Wa kaanoo yaqooloona a'izaa mitnaa wa kunnaa turaabanw wa izaaman'ainnaa lamab'oosoon

    Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

  48. 56:48

    أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ

    Awa aabaaa'unal awwaloon

    "Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

  49. 56:49

    قُلْ إِنَّ ٱلْأَوَّلِينَ وَٱلْءَاخِرِينَ

    Qul innal awwaleena wal aakhireen

    Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

  50. 56:50

    لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَٰتِ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ

    Lamajmoo'oona ilaa meeqaati yawmim ma'loon

    "Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

  51. 56:51

    ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ

    summa innakum ayyuhad daaalloonal mukazziboon

    "Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

  52. 56:52

    لَءَاكِلُونَ مِن شَجَرٍۢ مِّن زَقُّومٍۢ

    La aakiloona min shaja rim min zaqqoom

    "Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

  53. 56:53

    فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ

    Famaali'oona minhal butoon

    "Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

  54. 56:54

    فَشَٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ

    Fashaariboona 'alaihi minal hameem

    "Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

  55. 56:55

    فَشَٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ

    Fashaariboona shurbal heem

    "Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

  56. 56:56

    هَٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ

    Haazaa nuzuluhum yawmad deen

    Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

  57. 56:57

    نَحْنُ خَلَقْنَٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ

    Nahnu khalaqnaakum falaw laa tusaddiqoon

    Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

  58. 56:58

    أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ

    Afara'aytum maa tumnoon

    Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

  59. 56:59

    ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَٰلِقُونَ

    'A-antum takhluqoo nahooo am nahnul khaaliqoon

    Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

  60. 56:60

    نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ

    Nahnu qaddarnaa baina kumul mawta wa maa nahnu bimasbooqeen

    Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

  61. 56:61

    عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ

    'Alaaa an nubaddila amsaalakum wa nunshi'akum fee maa laa ta'lamoon

    A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

  62. 56:62

    وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ

    Wa laqad 'alimtumun nash atal oolaa falaw laa tazakkaroon

    Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

  63. 56:63

    أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ

    Afara'aytum maa tahrusoon

    Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

  64. 56:64

    ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ

    'A-antum tazra'oonahooo am nahnuz zaari'ooon

    Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

  65. 56:65

    لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَٰهُ حُطَٰمًۭا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ

    Law nashaaa'u laja'al naahu hutaaman fazaltum tafakkahoon

    Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

  66. 56:66

    إِنَّا لَمُغْرَمُونَ

    Innaa lamughramoon

    (Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

  67. 56:67

    بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ

    Bal nahnu mahroomoon

    "Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

  68. 56:68

    أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ

    Afara'aytumul maaa'allazee tashraboon

    Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

  69. 56:69

    ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ

    'A-antum anzaltumoohu minal muzni am nahnul munziloon

    Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

  70. 56:70

    لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَٰهُ أُجَاجًۭا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ

    Law nashaaa'u ja'alnaahu ujaajan falaw laa tashkuroon

    Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

  71. 56:71

    أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ

    Afara'aytumun naaral latee tooroon

    Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

  72. 56:72

    ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ

    'A-antum anshaatum shajaratahaaa am nahnul munshi'oon

    Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

  73. 56:73

    نَحْنُ جَعَلْنَٰهَا تَذْكِرَةًۭ وَمَتَٰعًۭا لِّلْمُقْوِينَ

    Nahnu ja'alnaahaa tazkira tanw wa mataa'al lilmuqween

    Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

  74. 56:74

    فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

    Fasabbih bismi Rabbikal 'azeem

    Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

  75. 56:75

    ۞ فَلَآ أُقْسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ

    Falaa uqsimu bimaawaa qi'innujoom

    To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.

  76. 56:76

    وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٌۭ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ

    Wa innahoo laqasamul lawta'lamoona'azeem

    Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.

  77. 56:77

    إِنَّهُۥ لَقُرْءَانٌۭ كَرِيمٌۭ

    Innahoo la quraanun kareem

    Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

  78. 56:78

    فِى كِتَٰبٍۢ مَّكْنُونٍۢ

    Fee kitaabim maknoon

    A cikin wani littafi tsararre.

  79. 56:79

    لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلْمُطَهَّرُونَ

    Laa yamassuhooo illal mutahharoon

    Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

  80. 56:80

    تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

    Tanzeelum mir Rabbil'aalameen

    Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

  81. 56:81

    أَفَبِهَٰذَا ٱلْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ

    Afabihaazal hadeesi antum mudhinoon

    Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

  82. 56:82

    وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ

    Wa taj'aloona rizqakum annakum tukazziboon

    Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

  83. 56:83

    فَلَوْلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلْحُلْقُومَ

    Falaw laaa izaa balaghatil hulqoom

    To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

  84. 56:84

    وَأَنتُمْ حِينَئِذٍۢ تَنظُرُونَ

    Wa antum heena'izin tanzuroon

    Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

  85. 56:85

    وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ

    Wa nahnu aqrabu ilaihi minkum wa laakil laa tubsiroon

    Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

  86. 56:86

    فَلَوْلَآ إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ

    Falaw laaa in kuntum ghira madeeneen

    To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

  87. 56:87

    تَرْجِعُونَهَآ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ

    Tarji'oonahaaa in kuntum saadiqeen

    Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

  88. 56:88

    فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ

    Fa ammaaa in kaana minal muqarrabeen

    To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

  89. 56:89

    فَرَوْحٌۭ وَرَيْحَانٌۭ وَجَنَّتُ نَعِيمٍۢ

    Farawhunw wa raihaa nunw wa jannatu na'eem

    Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

  90. 56:90

    وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنْ أَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ

    Wa ammaaa in kaana min as haabil yameen

    Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

  91. 56:91

    فَسَلَٰمٌۭ لَّكَ مِنْ أَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ

    Fasalaamul laka min as haabil yameen

    Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

  92. 56:92

    وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ

    Wa ammaaa in kaana minal mukazzibeenad daaalleen

    Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

  93. 56:93

    فَنُزُلٌۭ مِّنْ حَمِيمٍۢ

    Fanuzulum min hameem

    Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

  94. 56:94

    وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ

    Wa tasliyatu jaheem

    Da ƙõnuwa da Jahĩm,

  95. 56:95

    إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلْيَقِينِ

    Inna haaza lahuwa haqqul yaqeen

    Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

  96. 56:96

    فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

    Fasabbih bismi rabbikal 'azeem

    Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.

About Surah Al-Waqi'ah

Al-Waqi'ah, the Inevitable, describes the Day of Judgment when people will be sorted into three groups: those brought near, the people of the right, and the people of the left. It paints clear pictures of reward and loss, then points to the food we eat, the water we drink, and the fire we kindle as signs of the Creator's power.

Themes: The three groups, Reward and loss, Signs of the Creator, The Day of Judgment

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.