All Surahs

Surah An-Najm (undefined)

سُورَةُ النَّجۡمِ

Surah 53 of the Holy Quran · Meccan · 62 verses

Also spelled: Najm, An Najm, AnNajm, The Star

Surah An-Najm (undefined) is the 53th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 62 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 53:1

    وَٱلنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ

    Wannajmi izaa hawaa

    Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.

  2. 53:2

    مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ

    Maa dalla saahibukum wa maa ghawaa

    Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.

  3. 53:3

    وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلْهَوَىٰٓ

    Wa maa yyantiqu 'anilhawaaa

    Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.

  4. 53:4

    إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْىٌۭ يُوحَىٰ

    In huwa illaa Wahyuny yoohaa

    (Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.

  5. 53:5

    عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلْقُوَىٰ

    'Allamahoo shadeedul quwaa

    (Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.

  6. 53:6

    ذُو مِرَّةٍۢ فَٱسْتَوَىٰ

    Zoo mirratin fastawaa

    Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.

  7. 53:7

    وَهُوَ بِٱلْأُفُقِ ٱلْأَعْلَىٰ

    Wa huwa bil ufuqil a'laa

    Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.

  8. 53:8

    ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ

    Summa danaa fatadalla

    Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.

  9. 53:9

    فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ

    Fakaana qaaba qawsaini aw adnaa

    Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.

  10. 53:10

    فَأَوْحَىٰٓ إِلَىٰ عَبْدِهِۦ مَآ أَوْحَىٰ

    Fa awhaaa ilaa 'abdihee maaa awhaa

    Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).

  11. 53:11

    مَا كَذَبَ ٱلْفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ

    Maa kazabal fu'aadu maa ra aa

    Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.

  12. 53:12

    أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ

    Afatumaaroonahoo 'alaa maayaraa

    Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?

  13. 53:13

    وَلَقَدْ رَءَاهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ

    Wa laqad ra aahu nazlatan ukhraa

    Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.

  14. 53:14

    عِندَ سِدْرَةِ ٱلْمُنتَهَىٰ

    'Inda sidratil muntaha

    A wurin da magaryar tuƙẽwa take.

  15. 53:15

    عِندَهَا جَنَّةُ ٱلْمَأْوَىٰٓ

    'Indahaa jannatul maawaa

    A inda taken, nan Aljannar makoma take.

  16. 53:16

    إِذْ يَغْشَى ٱلسِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ

    Iz yaghshas sidrata maa yaghshaa

    Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.

  17. 53:17

    مَا زَاغَ ٱلْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ

    Maa zaaghal basaru wa maa taghaa

    Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.

  18. 53:18

    لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلْكُبْرَىٰٓ

    Laqad ra aa min aayaati Rabbihil kubraaa

    Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.

  19. 53:19

    أَفَرَءَيْتُمُ ٱللَّٰتَ وَٱلْعُزَّىٰ

    Afara'aytumul laata wal 'uzzaa

    Shin, kun ga Lãta da uzza?

  20. 53:20

    وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلْأُخْرَىٰٓ

    Wa manaatas saalisatal ukhraa

    Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?

  21. 53:21

    أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلْأُنثَىٰ

    A-lakumuz zakaru wa lahul unsaa

    Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?

  22. 53:22

    تِلْكَ إِذًۭا قِسْمَةٌۭ ضِيزَىٰٓ

    Tilka izan qismatun deezaa

    Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.

  23. 53:23

    إِنْ هِىَ إِلَّآ أَسْمَآءٌۭ سَمَّيْتُمُوهَآ أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَٰنٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهْوَى ٱلْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلْهُدَىٰٓ

    In hiya illaaa asmaaa'un sammaitumoohaaa antum wa aabaaa'ukum maaa anzalal laahu bihaa min sultaan; inyyattabi'oona illaz zanna wa maa tahwal anfusu wa laqad jaaa'ahum mir Rabbihimul hudaa

    Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).

  24. 53:24

    أَمْ لِلْإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ

    Am lil insaani maa taman naa

    Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?

  25. 53:25

    فَلِلَّهِ ٱلْءَاخِرَةُ وَٱلْأُولَىٰ

    Falillaahil aakhiratu wal oolaa

    To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).

  26. 53:26

    ۞ وَكَم مِّن مَّلَكٍۢ فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغْنِى شَفَٰعَتُهُمْ شَيْـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعْدِ أَن يَأْذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرْضَىٰٓ

    Wa kam mim malakin fissamaawaati laa tughnee shafaa'atuhum shai'an illaa mim ba'di anyyaazanal laahu limany yashaaa'u wa yardaa

    Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.

  27. 53:27

    إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِٱلْءَاخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ تَسْمِيَةَ ٱلْأُنثَىٰ

    innal lazeena laa yu'minoona bil aakhirati la yusammoonal malaaa'ikata tasmiyatal unsaa

    Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.

  28. 53:28

    وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ ۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغْنِى مِنَ ٱلْحَقِّ شَيْـًۭٔا

    Wa maa lahum bihee min 'ilmin iny yattabi'oona illaz zanna wa innaz zanna laa yughnee minal haqqi shai'aa

    Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.

  29. 53:29

    فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا

    Fa a'rid 'am man tawallaa 'an zikrinaa wa lam yurid illal hayaatad dunyaa

    Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).

  30. 53:30

    ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ ٱلْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ ٱهْتَدَىٰ

    Zalika mablaghuhum minal 'ilm; inna rabbaka huwa a'lamu biman dalla 'an sabee lihee wa huwa a'lamu bimanih tadaa

    Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.

  31. 53:31

    وَلِلَّهِ مَا فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِى ٱلْأَرْضِ لِيَجْزِىَ ٱلَّذِينَ أَسَٰٓـُٔوا۟ بِمَا عَمِلُوا۟ وَيَجْزِىَ ٱلَّذِينَ أَحْسَنُوا۟ بِٱلْحُسْنَى

    Wa lillaahi maa fis samaawaati wa maa fil ardi liyajziyal lazeena asaaa'oo bimaa 'amiloo wa yajziyal lazeena ahsanoo bilhusnaa

    Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.

  32. 53:32

    ٱلَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَٰٓئِرَ ٱلْإِثْمِ وَٱلْفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌۭ فِى بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوٓا۟ أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ

    Allazeena yajtaniboona kabaaa'iral ismi walfawaa hisha illal lamam; inna rabbaka waasi'ul maghfirah; huwa a'lamu bikum iz ansha akum minal ardi wa iz antum ajinnatun fee butooni umma haatikum falaa tuzakkooo anfusakum huwa a'lamu bimanit taqaa

    Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.

  33. 53:33

    أَفَرَءَيْتَ ٱلَّذِى تَوَلَّىٰ

    Afara'ayatal lazee tawallaa

    Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?

  34. 53:34

    وَأَعْطَىٰ قَلِيلًۭا وَأَكْدَىٰٓ

    Wa a'taa qaleelanw wa akdaa

    Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?

  35. 53:35

    أَعِندَهُۥ عِلْمُ ٱلْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ

    A'indahoo 'ilmul ghaibi fahuwa yaraa

    Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?

  36. 53:36

    أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِى صُحُفِ مُوسَىٰ

    Am lam yunabbaa bimaa fee suhuhfi Moosa

    Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?

  37. 53:37

    وَإِبْرَٰهِيمَ ٱلَّذِى وَفَّىٰٓ

    Wa Ibraaheemal lazee waffaaa

    Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?

  38. 53:38

    أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌۭ وِزْرَ أُخْرَىٰ

    Allaa taziru waaziratunw wizra ukhraa

    Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.

  39. 53:39

    وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ

    Wa al laisa lil insaani illaa maa sa'aa

    Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.

  40. 53:40

    وَأَنَّ سَعْيَهُۥ سَوْفَ يُرَىٰ

    Wa anna sa'yahoo sawfa yuraa

    Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.

  41. 53:41

    ثُمَّ يُجْزَىٰهُ ٱلْجَزَآءَ ٱلْأَوْفَىٰ

    Summa yujzaahul jazaaa 'al awfaa

    Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?

  42. 53:42

    وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلْمُنتَهَىٰ

    Wa anna ilaa rabbikal muntahaa

    Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?

  43. 53:43

    وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ

    Wa annahoo huwa adhaka wa abkaa

    Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.

  44. 53:44

    وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا

    Wa annahoo huwa amaata wa ahyaa

    Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.

  45. 53:45

    وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰ

    Wa annahoo khalaqaz zawjainiz zakara wal unsaa

    Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.

  46. 53:46

    مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ

    Min nutfatin izaa tumnaa

    Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.

  47. 53:47

    وَأَنَّ عَلَيْهِ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُخْرَىٰ

    Wa anna 'alaihin nash atal ukhraa

    Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.

  48. 53:48

    وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ

    Wa annahoo huwa aghnaa wa aqnaa

    Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.

  49. 53:49

    وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعْرَىٰ

    Wa annahoo huwa rabbush shi'raa

    Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.

  50. 53:50

    وَأَنَّهُۥٓ أَهْلَكَ عَادًا ٱلْأُولَىٰ

    Wa annahooo ahlak a 'Aadanil oolaa

    Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.

  51. 53:51

    وَثَمُودَا۟ فَمَآ أَبْقَىٰ

    Wa samooda famaaa abqaa

    Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.

  52. 53:52

    وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ

    Wa qawma Noohim min qablu innahum kaanoo hum azlama wa atghaa

    Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.

  53. 53:53

    وَٱلْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ

    Wal mu'tafikata ahwaa

    Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.

  54. 53:54

    فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ

    Faghashshaahaa maa ghashshaa

    Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.

  55. 53:55

    فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ

    Fabi ayyi aalaaa'i Rabbika tatamaaraa

    To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?

  56. 53:56

    هَٰذَا نَذِيرٌۭ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلْأُولَىٰٓ

    Haazaa nazeerum minan nuzuril oolaa

    wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.

  57. 53:57

    أَزِفَتِ ٱلْءَازِفَةُ

    Azifatil laazifah

    Makusanciya fa, tã yi kusa.

  58. 53:58

    لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ

    Laisa lahaa min doonil laahi kaashifah

    Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.

  59. 53:59

    أَفَمِنْ هَٰذَا ٱلْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ

    Afamin hazal hadeesi ta'jaboon

    Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?

  60. 53:60

    وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ

    Wa tadhakoona wa laa tabkoon

    Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?

  61. 53:61

    وَأَنتُمْ سَٰمِدُونَ

    Wa antum saamidoon

    Alhãli kunã mãsu wãsã?

  62. 53:62

    فَٱسْجُدُوا۟ لِلَّهِ وَٱعْبُدُوا۟ ۩

    Fasjudoo lillaahi wa'budoo

    To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).

About Surah An-Najm

An-Najm, the Star, opens by affirming that the Prophet (peace be upon him) did not speak from desire, but conveyed revelation. It refers to the ascension and the limits of human knowledge, and rejects the false idols people had invented. It reminds everyone that each person carries their own burden and is rewarded for their own effort.

Themes: Truth of revelation, Rejecting false idols, Personal accountability, Effort and reward

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.