All Surahs

Surah Abasa (undefined)

سُورَةُ عَبَسَ

Surah 80 of the Holy Quran · Meccan · 42 verses

Also spelled: He Frowned

Surah Abasa (undefined) is the 80th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 42 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 80:1

    عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ

    'Abasa wa tawallaa.

    Yã game huska kuma ya jũya bãya.

  2. 80:2

    أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ

    An jaa-ahul 'a-maa

    Sabõda makãho yã je masa.

  3. 80:3

    وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ

    Wa maa yudreeka la'allahu yaz zakkaa.

    To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

  4. 80:4

    أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ

    Au yaz zak karu fatanfa 'ahuz zikraa.

    Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

  5. 80:5

    أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ

    Amma manis taghnaa

    Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

  6. 80:6

    فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ

    Fa-anta lahu tasaddaa

    Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

  7. 80:7

    وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ

    Wa ma 'alaika allaa yaz zakka.

    To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

  8. 80:8

    وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ

    Wa amma man jaa-aka yas'a

    Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

  9. 80:9

    وَهُوَ يَخْشَىٰ

    Wahuwa yakhshaa,

    Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

  10. 80:10

    فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ

    Fa-anta 'anhu talah haa.

    Kai kuma kã shagala ga barinsa!

  11. 80:11

    كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌۭ

    Kalla innaha tazkirah

    A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

  12. 80:12

    فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

    Faman shaa a zakarah

    Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

  13. 80:13

    فِى صُحُفٍۢ مُّكَرَّمَةٍۢ

    Fi suhufim mukar rama,

    (Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

  14. 80:14

    مَّرْفُوعَةٍۢ مُّطَهَّرَةٍۭ

    Marfoo'atim mutah hara,

    Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

  15. 80:15

    بِأَيْدِى سَفَرَةٍۢ

    Bi'aidee safara

    A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

  16. 80:16

    كِرَامٍۭ بَرَرَةٍۢ

    Kiraamim bararah.

    Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

  17. 80:17

    قُتِلَ ٱلْإِنسَٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ

    Qutilal-insanu maa akfarah.

    An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

  18. 80:18

    مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ

    Min aiyyi shai-in Khalaq

    Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

  19. 80:19

    مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ

    Min nutfah; khalaqahu faqad-darah.

    Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

  20. 80:20

    ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ

    Thummas sabeela yas-sarah

    Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

  21. 80:21

    ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ

    Thumma amatahu fa-aqbarah

    Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

  22. 80:22

    ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

    Thumma iza shaa-a ansharah

    Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

  23. 80:23

    كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ

    Kalla lamma yaqdi maa amarah.

    Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

  24. 80:24

    فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ

    Falyanzuril insanu ilaa ta-amih

    To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

  25. 80:25

    أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّۭا

    Anna sabab nalmaa-a sabba.

    Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

  26. 80:26

    ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّۭا

    Thumma sha qaqnal-arda shaqqa.

    Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

  27. 80:27

    فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّۭا

    Fa ambatna feeha habba

    Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

  28. 80:28

    وَعِنَبًۭا وَقَضْبًۭا

    Wa 'inabaw-wa qadba

    Da inabi da ciyãwa.

  29. 80:29

    وَزَيْتُونًۭا وَنَخْلًۭا

    Wa zaitoonaw wanakh la'

    Da zaitũni da itãcen dabĩno.

  30. 80:30

    وَحَدَآئِقَ غُلْبًۭا

    Wa hadaa-iqa ghulba

    Da lambuna, mãsu yawan itãce.

  31. 80:31

    وَفَٰكِهَةًۭ وَأَبًّۭا

    Wa faki hataw-wa abba.

    Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

  32. 80:32

    مَّتَٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ

    Mata'al-lakum wa li-an'amikum.

    Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

  33. 80:33

    فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

    Faiza jaa-atis saakhah.

    To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

  34. 80:34

    يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

    Yauma yafir-rul mar-u min akheeh

    Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

  35. 80:35

    وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

    Wa ummihee wa abeeh

    Da uwarsa da ubansa.

  36. 80:36

    وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

    Wa sahi batihee wa baneeh.

    Da mãtarsa da ɗiyansa.

  37. 80:37

    لِكُلِّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍۢ شَأْنٌۭ يُغْنِيهِ

    Likul limri-im-minuhm yaumaa-izin shaa nuy-yughneeh

    Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

  38. 80:38

    وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ مُّسْفِرَةٌۭ

    Wujoo huny-yauma-izim-musfira;

    Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

  39. 80:39

    ضَاحِكَةٌۭ مُّسْتَبْشِرَةٌۭ

    Dahi katum mustab shirah

    Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

  40. 80:40

    وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌۭ

    Wa wujoohuy yauma-izin 'alaiha ghabar a

    Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

  41. 80:41

    تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

    Tarhaquha qatarah.

    Baƙi zai rufe su.

  42. 80:42

    أُو۟لَٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ

    Ulaa-ika humul-kafa ratul-fajarah.

    Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

About Surah Abasa

Abasa, He Frowned, opens by correcting a moment when a blind man seeking guidance was overlooked in favor of the powerful, teaching that sincerity matters more than status. It then points to the human's own creation and the food that grows from the earth as reasons for gratitude and humility before Allah.

Themes: Sincerity over status, Humility, Gratitude, Reflection on creation

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.