Surah An-Nazi'at (undefined) is the 79th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 46 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 79:1
وَٱلنَّٰزِعَٰتِ غَرْقًۭا
Wan naazi 'aati gharqa
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
- 79:2
وَٱلنَّٰشِطَٰتِ نَشْطًۭا
Wan naa shi taati nashta
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
- 79:3
وَٱلسَّٰبِحَٰتِ سَبْحًۭا
Wass saabi-haati sabha
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
- 79:4
فَٱلسَّٰبِقَٰتِ سَبْقًۭا
Fass saabi qaati sabqa
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
- 79:5
فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا
Fal mu dab-bi raati amra
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
- 79:6
يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
Yawma tarjufur raajifa
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
- 79:7
تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
Tatba'u har raadifa
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
- 79:8
قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ
Quloobuny-yau maaiziw-waaji-fa
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
- 79:9
أَبْصَٰرُهَا خَٰشِعَةٌۭ
Absaa ruhaa khashi'ah
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
- 79:10
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ
Ya qoo loona a-inna lamar doo doona fil haafirah
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
- 79:11
أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمًۭا نَّخِرَةًۭ
Aizaa kunna 'izaa man-nakhirah
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
- 79:12
قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ
Qaalu tilka izan karratun khaasirah.
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
- 79:13
فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ
Fa inna ma hiya zajratuw-waahida
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
- 79:14
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
Faizaa hum biss saahirah
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
- 79:15
هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
Hal ataaka hadeethu Musaa
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
- 79:16
إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى
Iz nadaahu rabbuhu bil waadil-muqad dasi tuwa
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
- 79:17
ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
Izhab ilaa fir'auna innahu taghaa.
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
- 79:18
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
Faqul hal laka ilaa-an tazakka.
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
- 79:19
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ
Wa ahdi yaka ila rabbika fatakh sha
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
- 79:20
فَأَرَىٰهُ ٱلْءَايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ
Fa araahul-aayatal kubra.
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
- 79:21
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
Fa kazzaba wa asaa.
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
- 79:22
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ
Thumma adbara yas'aa.
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
- 79:23
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
Fa hashara fanada.
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
- 79:24
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ
Faqala ana rabbu kumul-a'laa.
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
- 79:25
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْءَاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ
Fa-akha zahul laahu nakalal aakhirati wal-oola.
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
- 79:26
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ
Inna fee zaalika la'ibratal limaiy-yaksha
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
- 79:27
ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا
A-antum a shaddu khalqan amis samaa-u banaaha.
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
- 79:28
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا
Raf'a sam kaha fasaw waaha
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
- 79:29
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا
Wa aghtasha lailaha wa akhraja duhaaha.
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
- 79:30
وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
Wal arda b'ada zaalika dahaaha.
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
- 79:31
أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا
Akhraja minha maa-aha wa mar 'aaha.
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
- 79:32
وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا
Wal jibala arsaaha.
Da duwatsu, Yã kafe ta.
- 79:33
مَتَٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ
Mataa'al lakum wali an 'aamikum.
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
- 79:34
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ
Fa-izaa jaaa'atit taaam matul kubraa.
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
- 79:35
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ
Yauma Yata zakkarul insaanu ma sa'aa.
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
- 79:36
وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
Wa burrizatil-jaheemu limany-yaraa.
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
- 79:37
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
Fa ammaa man taghaa.
To, amma wanda ya yi girman kai.
- 79:38
وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
Wa aasaral hayaatad dunyaa
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
- 79:39
فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
Fa innal jaheema hiyal maawaa.
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
- 79:40
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ
Wa ammaa man khaafa maqaama Rabbihee wa nahan nafsa 'anil hawaa
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
- 79:41
فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
Fa innal jannata hiyal maawaa
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
- 79:42
يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا
Yas'aloonaka 'anis saa'ati ayyaana mursaahaa
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
- 79:43
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ
Feema anta min zikraahaa
Me ya haɗã ka da ambatonta?
- 79:44
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
Ilaa Rabbika muntahaa haa
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
- 79:45
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا
Innamaaa anta munziru maiy yakshaahaa
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
- 79:46
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا
Ka annahum Yawma yarawnahaa lam yalbasooo illaa 'ashiyyatan aw duhaahaa
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
About Surah An-Nazi'at
An-Nazi'at, Those Who Drag Forth, opens with oaths about the angels who carry out Allah's command. It recalls the story of Musa and Pharaoh as a warning, then turns to the building of the heavens and the spreading of the earth as proof of resurrection. It closes by reminding people that the Hour's timing rests with Allah alone.
Themes: The angels, Musa and Pharaoh, Signs of resurrection, The Hour
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.