Surah At-Takwir (undefined) is the 81th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 29 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 81:1
إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Izash shamsu kuwwirat
Idan rãna aka shafe haskenta
- 81:2
وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ
Wa izan nujoomun kadarat
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
- 81:3
وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ
Wa izal jibaalu suyyirat
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
- 81:4
وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ
Wa izal 'ishaaru 'uttilat
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
- 81:5
وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ
Wa izal wuhooshu hushirat
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
- 81:6
وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ
Wa izal bihaaru sujjirat
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
- 81:7
وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ
Wa izan nufoosu zuwwijat
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
- 81:8
وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ
Wa izal maw'oodatu su'ilat
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
- 81:9
بِأَىِّ ذَنۢبٍۢ قُتِلَتْ
Bi ayyi zambin qutilat
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
- 81:10
وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ
Wa izas suhufu nushirat
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
- 81:11
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ
Wa izas samaaa'u kushitat
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
- 81:12
وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
Wa izal jaheemu su'-'irat
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
- 81:13
وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
Wa izal jannatu uzlifat
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
- 81:14
عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّآ أَحْضَرَتْ
'Alimat nafsum maaa ahdarat
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
- 81:15
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ
Falaaa uqsimu bil khunnas
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
- 81:16
ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ
Al jawaaril kunnas
Mãsu gudu suna ɓũya.
- 81:17
وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
Wallaili izaa 'as'as
Da dare idan ya bãyar da bãya.
- 81:18
وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Wassubhi izaa tanaffas
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
- 81:19
إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ
Innahoo laqawlu rasoolin kareem
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
- 81:20
ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍۢ
Zee quwwatin 'inda zil 'arshi makeen
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
- 81:21
مُّطَاعٍۢ ثَمَّ أَمِينٍۢ
Mutaa'in samma ameen
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
- 81:22
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍۢ
Wa maa saahibukum bimajnoon
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
- 81:23
وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ
Wa laqad ra aahu bilufuqil mubeen
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
- 81:24
وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍۢ
Wa maa huwa 'alal ghaibi bidaneen
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
- 81:25
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَٰنٍۢ رَّجِيمٍۢ
Wa maa huwa biqawli shaitaanir rajeem
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
- 81:26
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
Fa ayna tazhaboon
Shin, a inã zã ku tafi?
- 81:27
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَٰلَمِينَ
In huwa illaa zikrul lil'aalameen
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
- 81:28
لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
Liman shaaa'a minkum ai yastaqeem
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
- 81:29
وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَٰلَمِينَ
Wa maa tashaaa'oona illaaa ai yashaaa 'al laahu Rabbul 'Aalameen
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
About Surah At-Takwir
At-Takwir, the Overthrowing, describes the unraveling of the world at the end of time: the sun folded up, the stars falling, the seas set ablaze. It then affirms that the Quran is the word brought by a noble messenger, and that the Prophet (peace be upon him) was no madman but a true guide.
Themes: The end of the world, Truth of revelation, The noble messenger, Certainty
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.