Surah Ash-Shams (undefined) is the 91th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 15 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 91:1
وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا
Wash shamsi wa duhaa haa
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
- 91:2
وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا
Wal qamari izaa talaa haa
Kuma da wata idan ya bi ta.
- 91:3
وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا
Wannahaari izaa jallaa haa
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
- 91:4
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا
Wallaili izaa yaghshaa haa
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
- 91:5
وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا
Wassamaaa'i wa maa banaahaa
Da sama da abin da ya gina ta.
- 91:6
وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا
Wal ardi wa maa tahaahaa
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
- 91:7
وَنَفْسٍۢ وَمَا سَوَّىٰهَا
Wa nafsinw wa maa sawwaahaa
Da rai da abin da ya daidaita shi.
- 91:8
فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا
Fa-alhamahaa fujoorahaa wa taqwaahaa
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.
- 91:9
قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا
Qad aflaha man zakkaahaa
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.
- 91:10
وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا
Wa qad khaaba man dassaahaa
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.
- 91:11
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ
Kazzabat Samoodu bi taghwaahaaa
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
- 91:12
إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا
Izim ba'asa ashqaahaa
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
- 91:13
فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَٰهَا
Faqaala lahum Rasoolul laahi naaqatal laahi wa suqiyaahaa
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
- 91:14
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا
Fakazzaboohu fa'aqaroohaa fadamdama 'alaihim Rabbuhum bizambihim fasaw waahaa
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
- 91:15
وَلَا يَخَافُ عُقْبَٰهَا
Wa laa yakhaafu'uqbaahaa
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).
About Surah Ash-Shams
Ash-Shams, the Sun, opens with a series of oaths by the sun, the moon, the day, and the night, building to the central truth: that the one who purifies his soul succeeds, and the one who corrupts it fails. It recalls the people of Thamud who killed the she-camel and met their ruin.
Themes: Oaths by creation, Purifying the soul, Success and failure, The people of Thamud
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.