All Surahs

Surah Al-Balad (undefined)

سُورَةُ البَلَدِ

Surah 90 of the Holy Quran · Meccan · 20 verses

Also spelled: Balad, Al Balad, AlBalad, The City

Surah Al-Balad (undefined) is the 90th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 20 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 90:1

    لَآ أُقْسِمُ بِهَٰذَا ٱلْبَلَدِ

    Laaa uqsimu bihaazal balad

    Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

  2. 90:2

    وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَٰذَا ٱلْبَلَدِ

    Wa anta hillum bihaazal balad

    Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

  3. 90:3

    وَوَالِدٍۢ وَمَا وَلَدَ

    Wa waalidinw wa maa walad

    Da mahaifi da abin da ya haifa.

  4. 90:4

    لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَٰنَ فِى كَبَدٍ

    Laqad khalaqnal insaana fee kabad

    Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

  5. 90:5

    أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌۭ

    Ayahsabu al-lai yaqdira 'alaihi ahad

    Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

  6. 90:6

    يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًۭا لُّبَدًا

    Yaqoolu ahlaktu maalal lubadaa

    Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

  7. 90:7

    أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ

    Ayahsabu al lam yarahooo ahad

    Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

  8. 90:8

    أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ

    Alam naj'al lahoo 'aynayn

    Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

  9. 90:9

    وَلِسَانًۭا وَشَفَتَيْنِ

    Wa lisaananw wa shafatayn

    Da harshe, da leɓɓa biyu.

  10. 90:10

    وَهَدَيْنَٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ

    Wa hadaynaahun najdayn

    Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

  11. 90:11

    فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ

    Falaq tahamal-'aqabah

    To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

  12. 90:12

    وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ

    Wa maaa adraaka mal'aqabah

    Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

  13. 90:13

    فَكُّ رَقَبَةٍ

    Fakku raqabah

    Ita ce fansar wuyan bãwa.

  14. 90:14

    أَوْ إِطْعَٰمٌۭ فِى يَوْمٍۢ ذِى مَسْغَبَةٍۢ

    Aw it'aamun fee yawmin zee masghabah

    Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

  15. 90:15

    يَتِيمًۭا ذَا مَقْرَبَةٍ

    Yateeman zaa maqrabah

    Ga marãya ma'abũcin zumunta.

  16. 90:16

    أَوْ مِسْكِينًۭا ذَا مَتْرَبَةٍۢ

    Aw miskeenan zaa matrabah

    Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

  17. 90:17

    ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ

    Summa kaana minal lazeena aamanoo wa tawaasaw bissabri wa tawaasaw bilmarhamah

    Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

  18. 90:18

    أُو۟لَٰٓئِكَ أَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ

    Ulaaa'ika As-haabul maimanah

    Waɗannan ne ma'abũta albarka

  19. 90:19

    وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا هُمْ أَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ

    Wallazeena kafaroo bi aayaatinaa hum as-haabul Mash'amah

    Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

  20. 90:20

    عَلَيْهِمْ نَارٌۭ مُّؤْصَدَةٌۢ

    Alaihim naarum mu'sadah

    A kansu akwai wata wuta abar kullewa.

About Surah Al-Balad

Al-Balad, the City, swears by the city of Makkah and reminds the human being that they were created to face struggle. It describes the steep path of righteousness as freeing a slave, feeding the hungry, the orphan, and the poor, and being among those who believe and encourage one another to patience and compassion.

Themes: Life as struggle, The steep path, Feeding the needy, Compassion

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.