Surah Al-Qiyamah (undefined) is the 75th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 40 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 75:1
لَآ أُقْسِمُ بِيَوْمِ ٱلْقِيَٰمَةِ
Laaa uqsimu bi yawmil qiyaamah
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
- 75:2
وَلَآ أُقْسِمُ بِٱلنَّفْسِ ٱللَّوَّامَةِ
Wa laaa uqsimu bin nafsil lawwaamah
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
- 75:3
أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُۥ
Ayahsabul insaanu al lan najm'a 'izaamah
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
- 75:4
بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّىَ بَنَانَهُۥ
Balaa qaadireena 'alaaa an nusawwiya banaanah
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
- 75:5
بَلْ يُرِيدُ ٱلْإِنسَٰنُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُۥ
Bal yureedul insaanu liyafjura amaamah
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
- 75:6
يَسْـَٔلُ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلْقِيَٰمَةِ
Yas'alu ayyyaana yawmul qiyaamah
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
- 75:7
فَإِذَا بَرِقَ ٱلْبَصَرُ
Fa izaa bariqal basar
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
- 75:8
وَخَسَفَ ٱلْقَمَرُ
We khasafal qamar
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
- 75:9
وَجُمِعَ ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ
Wa jumi'ash shamusu wal qamar
Aka tãra rãnã da watã
- 75:10
يَقُولُ ٱلْإِنسَٰنُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ ٱلْمَفَرُّ
Yaqoolul insaanu yaw ma 'izin aynal mafarr
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
- 75:11
كَلَّا لَا وَزَرَ
Kallaa laa wazar
A'aha! bãbu mafaka.
- 75:12
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمُسْتَقَرُّ
Ilaa rabbika yawma 'izinil mustaqarr
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
- 75:13
يُنَبَّؤُا۟ ٱلْإِنسَٰنُ يَوْمَئِذٍۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ
Yunabba 'ul insaanu yawma 'izim bimaa qaddama wa akhkhar
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
- 75:14
بَلِ ٱلْإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفْسِهِۦ بَصِيرَةٌۭ
Balil insaanu 'alaa nafsihee baseerah
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
- 75:15
وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ
Wa law alqaa ma'aazeerah
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
- 75:16
لَا تُحَرِّكْ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِۦٓ
Laa tuharrik bihee lisaa naka lita'jala bih
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
- 75:17
إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُۥ وَقُرْءَانَهُۥ
Inna 'alainaa jam'ahoo wa qur aanah
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
- 75:18
فَإِذَا قَرَأْنَٰهُ فَٱتَّبِعْ قُرْءَانَهُۥ
Fa izaa qaraanaahu fattabi' qur aanah
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
- 75:19
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُۥ
Summa inna 'alainaa bayaanah
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
- 75:20
كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ ٱلْعَاجِلَةَ
Kallaa bal tuhibboonal 'aajilah
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
- 75:21
وَتَذَرُونَ ٱلْءَاخِرَةَ
Wa tazaroonal Aakhirah
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
- 75:22
وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاضِرَةٌ
Wujoohuny yawma 'izin naadirah
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
- 75:23
إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌۭ
Ilaa rabbihaa naazirah
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
- 75:24
وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۭ بَاسِرَةٌۭ
Wa wujoohuny yawma 'izim baasirah
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
- 75:25
تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌۭ
Tazunnu any yuf'ala bihaa faaqirah
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
- 75:26
كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِىَ
Kallaaa izaa balaghatit taraaqee
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
- 75:27
وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍۢ
Wa qeela man raaq
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
- 75:28
وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلْفِرَاقُ
Wa zanna annahul firaaq
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
- 75:29
وَٱلْتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ
Waltaffatis saaqu bissaaq
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
- 75:30
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمَسَاقُ
Ilaa rabbika yawma'izinil masaaq
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
- 75:31
فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ
Falaa saddaqa wa laa sallaa
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
- 75:32
وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Wa laakin kazzaba wa tawalla
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
- 75:33
ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ
Summa zahaba ilaaa ahlihee yatamatta
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
- 75:34
أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ
Awlaa laka fa awlaa
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
- 75:35
ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰٓ
Summa awlaa laka fa awla
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
- 75:36
أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَٰنُ أَن يُتْرَكَ سُدًى
Ayahsabul insaanu anyytraka sudaa
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
- 75:37
أَلَمْ يَكُ نُطْفَةًۭ مِّن مَّنِىٍّۢ يُمْنَىٰ
Alam yaku nutfatam mim maniyyiny yumnaa
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
- 75:38
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةًۭ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ
Summa kaana 'alaqata fakhalaq fasawwaa
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
- 75:39
فَجَعَلَ مِنْهُ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ
Faja'ala minhuz zawjayniz zakara wal unsaa
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
- 75:40
أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحْۦِىَ ٱلْمَوْتَىٰ
Alaisa zaalika biqaadirin 'alaaa any yuhyiyal mawtaa
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?
About Surah Al-Qiyamah
Al-Qiyamah, the Resurrection, answers those who doubted that Allah could bring the dead back to life. It points out that Allah can reassemble even the tips of a person's fingers, describes the moment the eyes are dazzled and the soul reaches the throat, and reminds the human being that they were created for a purpose, not left without account.
Themes: The resurrection, Power of the Creator, The moment of death, Purpose
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.