Surah Al-Muddaththir (undefined) is the 74th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 56 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 74:1
يَٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ
Yaaa ayyuhal muddassir
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
- 74:2
قُمْ فَأَنذِرْ
Qum fa anzir
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
- 74:3
وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ
Wa rabbaka fakabbir
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
- 74:4
وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ
Wa siyaabaka fatahhir
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
- 74:5
وَٱلرُّجْزَ فَٱهْجُرْ
Warrujza fahjur
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
- 74:6
وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ
Wa laa tamnun tastaksir
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
- 74:7
وَلِرَبِّكَ فَٱصْبِرْ
Wa li Rabbika fasbir
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
- 74:8
فَإِذَا نُقِرَ فِى ٱلنَّاقُورِ
Fa izaa nuqira fin naaqoor
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
- 74:9
فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍۢ يَوْمٌ عَسِيرٌ
Fazaalika yawma 'iziny yawmun 'aseer
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
- 74:10
عَلَى ٱلْكَٰفِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍۢ
'Alal kaafireena ghayru yaseer
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
- 74:11
ذَرْنِى وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًۭا
Zamee wa man khalaqtu waheedaa
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
- 74:12
وَجَعَلْتُ لَهُۥ مَالًۭا مَّمْدُودًۭا
Wa ja'altu lahoo maalam mamdoodaa
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
- 74:13
وَبَنِينَ شُهُودًۭا
Wa baneena shuhoodaa
Da ɗiyã halartattu,
- 74:14
وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمْهِيدًۭا
Wa mahhattu lahoo tamheeda
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
- 74:15
ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ
Summa yat ma'u an azeed
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
- 74:16
كَلَّآ ۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِءَايَٰتِنَا عَنِيدًۭا
Kallaaa innahoo kaana li Aayaatinaa 'aneedaa
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
- 74:17
سَأُرْهِقُهُۥ صَعُودًا
Sa urhiquhoo sa'oodaa
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
- 74:18
إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ
Innahoo fakkara wa qaddar
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
- 74:19
فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
Faqutila kayfa qaddar
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
- 74:20
ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
Summa qutila kaifa qaddar
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
- 74:21
ثُمَّ نَظَرَ
Summa nazar
Sa'an nan, ya yi tunãni
- 74:22
ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ
Summa 'abasa wa basar
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
- 74:23
ثُمَّ أَدْبَرَ وَٱسْتَكْبَرَ
Summaa adbara wastakbar
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
- 74:24
فَقَالَ إِنْ هَٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ يُؤْثَرُ
Faqaala in haazaaa illaa sihruny yu'sar
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
- 74:25
إِنْ هَٰذَآ إِلَّا قَوْلُ ٱلْبَشَرِ
In haazaaa illaa qawlul bashar
"Wannan maganar mutum dai ce."
- 74:26
سَأُصْلِيهِ سَقَرَ
Sa usleehi saqar
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
- 74:27
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سَقَرُ
Wa maaa adraaka maa saqar
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
- 74:28
لَا تُبْقِى وَلَا تَذَرُ
Laa tubqee wa laa tazar
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
- 74:29
لَوَّاحَةٌۭ لِّلْبَشَرِ
Lawwaahatul lilbashar
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
- 74:30
عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ
'Alaihaa tis'ata 'ashar
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
- 74:31
وَمَا جَعَلْنَآ أَصْحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَٰٓئِكَةًۭ ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةًۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لِيَسْتَيْقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَٰبَ وَيَزْدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ إِيمَٰنًۭا ۙ وَلَا يَرْتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَٰبَ وَٱلْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِى قُلُوبِهِم مَّرَضٌۭ وَٱلْكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلًۭا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهْدِى مَن يَشَآءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِىَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ
Wa maaja''alnaaa As haaban naari illaa malaaa 'ikatanw wa maa ja'alnaa 'iddatahum illaa fitnatal lillazeena kafaroo liyastayqinal lazeena ootul kitaaba wa yazdaadal lazeena aamanooo eemaananw wa laa yartaabal lazeena ootul kitaaba walmu'minoona wa liyaqoolal lazeena fee quloo bihim maradunw walkaafiroona maazaaa araadal laahu bihaazaa masalaa; kazaalika yudillul laahu many yashaaa'u wa yahdee many yashaaa'; wa maa ya'lamu junooda rabbika illaa hoo; wa maa hiya illaa zikraa lil bashar
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.
- 74:32
كَلَّا وَٱلْقَمَرِ
Kallaa walqamar
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
- 74:33
وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ
Wallaili adbar
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
- 74:34
وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ
Wassub hi izaaa asfar
Da sãfiya idan ta wãye.
- 74:35
إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ
Innahaa la ihdal kubar
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
- 74:36
نَذِيرًۭا لِّلْبَشَرِ
Nazeeral lilbashar
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
- 74:37
لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ
Liman shaaa'a minkum any yataqaddama aw yata akhkhar
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
- 74:38
كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ
Kullu nafsim bim kasabat raheenah
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
- 74:39
إِلَّآ أَصْحَٰبَ ٱلْيَمِينِ
Illaaa as haabal yameen
Fãce mutãnen dãma.
- 74:40
فِى جَنَّٰتٍۢ يَتَسَآءَلُونَ
Fee jannaatiny yata saaa'aloon
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
- 74:41
عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ
'Anil mujrimeen
Game da mãsu laifi.
- 74:42
مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ
Maa salakakum fee saqar
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
- 74:43
قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ
Qaaloo lam naku minal musalleen
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
- 74:44
وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ
Wa lam naku nut'imul miskeen
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
- 74:45
وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ
Wa kunnaa nakhoodu ma'al khaaa'ideen
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
- 74:46
وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
Wa kunnaa nukazzibu bi yawmid Deen
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
- 74:47
حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ
Hattaaa ataanal yaqeen
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
- 74:48
فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَٰعَةُ ٱلشَّٰفِعِينَ
Famaa tanfa'uhum shafaa'atush shaafi'een
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
- 74:49
فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ
Famaa lahum 'anittazkirati mu'rideen
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
- 74:50
كَأَنَّهُمْ حُمُرٌۭ مُّسْتَنفِرَةٌۭ
Ka annahum humurum mustanfirah
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
- 74:51
فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ
Farrat min qaswarah
Sun gudu daga zãki.
- 74:52
بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًۭا مُّنَشَّرَةًۭ
Bal yureedu kullum ri'im minhum any yu'taa suhufam munashsharah
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
- 74:53
كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْءَاخِرَةَ
Kallaa bal laa yakhaafoonal aakhirah
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
- 74:54
كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌۭ
Kallaaa innahoo tazkirah
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
- 74:55
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
Fa man shaaa'a zakarah
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
- 74:56
وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ
Wa maa yazkuroona illaaa any yashaaa'al laah; Huwa ahlut taqwaa wa ahlul maghfirah
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.
About Surah Al-Muddaththir
Al-Muddaththir, the Cloaked One, contains some of the earliest revelation, calling the Prophet (peace be upon him) to rise and warn, to magnify his Lord, and to keep himself pure. It warns the arrogant who plotted against the message and describes the regret of those who neglected prayer and feeding the poor.
Themes: The call to warn, Purity, Arrogance and its end, Prayer and charity
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.