All Surahs

Surah Al-Qalam (undefined)

سُورَةُ القَلَمِ

Surah 68 of the Holy Quran · Meccan · 52 verses

Also spelled: Qalam, Al Qalam, AlQalam, The Pen

Surah Al-Qalam (undefined) is the 68th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 52 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 68:1

    نٓ ۚ وَٱلْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ

    Noon; walqalami wa maa yasturoon

    Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

  2. 68:2

    مَآ أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍۢ

    Maa anta bini'mati Rabbika bimajnoon

    Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

  3. 68:3

    وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍۢ

    Wa inna laka la ajran ghaira mamnoon

    Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

  4. 68:4

    وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍۢ

    Wa innaka la'alaa khuluqin 'azeem

    Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

  5. 68:5

    فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ

    Fasatubsiru wa yubsiroon

    Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

  6. 68:6

    بِأَييِّكُمُ ٱلْمَفْتُونُ

    Bi ayyikumul maftoon

    Ga wanenku haukã take.

  7. 68:7

    إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِٱلْمُهْتَدِينَ

    Innaa Rabbaka Huwa a'lamu biman dalla 'an sabeelihee wa Huwa a'lamu bilmuhtadeen

    Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

  8. 68:8

    فَلَا تُطِعِ ٱلْمُكَذِّبِينَ

    Falaa tuti'il mukazzibeen

    Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

  9. 68:9

    وَدُّوا۟ لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ

    Waddoo law tudhinu fa-yudhinoon

    Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

  10. 68:10

    وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍۢ مَّهِينٍ

    Wa laa tuti' kulla hallaa fim maheen

    Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

  11. 68:11

    هَمَّازٍۢ مَّشَّآءٍۭ بِنَمِيمٍۢ

    Hammaazim mash shaaa'im binameem

    Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

  12. 68:12

    مَّنَّاعٍۢ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ

    Mannaa'il lilkhairi mu'tadin aseem

    Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

  13. 68:13

    عُتُلٍّۭ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

    'Utullim ba'da zaalika zaneem

    Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

  14. 68:14

    أَن كَانَ ذَا مَالٍۢ وَبَنِينَ

    An kaana zaa maalinw-wa baneen

    Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

  15. 68:15

    إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ

    Izaa tutlaa 'alaihi aayaatunaa qaala asaateerul awwaleen

    Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

  16. 68:16

    سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلْخُرْطُومِ

    Sanasimuhoo 'alal khurtoom

    Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

  17. 68:17

    إِنَّا بَلَوْنَٰهُمْ كَمَا بَلَوْنَآ أَصْحَٰبَ ٱلْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا۟ لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ

    Innaa balawnaahum kamaa balawnaaa As-haabal jannati iz 'aqsamoo la-yasri munnahaa musbiheen

    Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

  18. 68:18

    وَلَا يَسْتَثْنُونَ

    Wa laa yastasnoon

    Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

  19. 68:19

    فَطَافَ عَلَيْهَا طَآئِفٌۭ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَآئِمُونَ

    Fataafa 'alaihaa taaa'i fum mir rabbika wa hum naaa'imoon

    Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

  20. 68:20

    فَأَصْبَحَتْ كَٱلصَّرِيمِ

    Fa asbahat kassareem

    Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

  21. 68:21

    فَتَنَادَوْا۟ مُصْبِحِينَ

    Fatanaadaw musbiheen

    Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

  22. 68:22

    أَنِ ٱغْدُوا۟ عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَٰرِمِينَ

    Anighdoo 'alaa harsikum in kuntum saarimeen

    Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

  23. 68:23

    فَٱنطَلَقُوا۟ وَهُمْ يَتَخَٰفَتُونَ

    Fantalaqoo wa hum yatakhaafatoon

    Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

  24. 68:24

    أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا ٱلْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌۭ

    Al laa yadkhulannahal yawma 'alaikum miskeen

    "Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

  25. 68:25

    وَغَدَوْا۟ عَلَىٰ حَرْدٍۢ قَٰدِرِينَ

    Wa ghadaw 'alaa hardin qaadireen

    Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

  26. 68:26

    فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوٓا۟ إِنَّا لَضَآلُّونَ

    Falammaa ra awhaa qaalooo innaa ladaaalloon

    Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

  27. 68:27

    بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ

    Bal nahnu mahroomoon

    "Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

  28. 68:28

    قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ

    Qaala awsatuhum alam aqul lakum law laa tusabbihoon

    Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

  29. 68:29

    قَالُوا۟ سُبْحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

    Qaaloo subhaana rabbinaaa innaa kunnaa zaalimeen

    Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

  30. 68:30

    فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَلَٰوَمُونَ

    Fa aqbala ba'duhum 'alaa ba'diny yatalaawamoon

    Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

  31. 68:31

    قَالُوا۟ يَٰوَيْلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ

    Qaaloo yaa wailanaaa innaa kunnaa taagheen

    Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

  32. 68:32

    عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًۭا مِّنْهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ

    'Asaa rabbunaaa any yubdilanaa khairam minhaaa innaaa ilaa rabbinaa raaghiboon

    "Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

  33. 68:33

    كَذَٰلِكَ ٱلْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ ٱلْءَاخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا۟ يَعْلَمُونَ

    Kazaalikal azaab, wa la'azaabul aakhirati akbar; law kaanoo ya'lamoon

    Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

  34. 68:34

    إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

    Inna lilmuttaqeena 'inda rabbihim jannaatin na'eem

    Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

  35. 68:35

    أَفَنَجْعَلُ ٱلْمُسْلِمِينَ كَٱلْمُجْرِمِينَ

    Afanaj'alul muslimeena kalmujrimeen

    Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

  36. 68:36

    مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

    Maa lakum kaifa tahhkumoon

    Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

  37. 68:37

    أَمْ لَكُمْ كِتَٰبٌۭ فِيهِ تَدْرُسُونَ

    Am lakum kitaabun feehi tadrusoon

    Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

  38. 68:38

    إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ

    Inna lakum feehi lamaa takhaiyaroon

    Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

  39. 68:39

    أَمْ لَكُمْ أَيْمَٰنٌ عَلَيْنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْقِيَٰمَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ

    Am lakum aymaanun 'alainaa baalighatun ilaa yawmil qiyaamati inna lakum lamaa tahkumoon

    Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

  40. 68:40

    سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ

    Salhum ayyuhum bizaa lika za'eem

    Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

  41. 68:41

    أَمْ لَهُمْ شُرَكَآءُ فَلْيَأْتُوا۟ بِشُرَكَآئِهِمْ إِن كَانُوا۟ صَٰدِقِينَ

    Am lahum shurakaaa'u falyaatoo bishurakaaa 'ihim in kaanoo saadiqeen

    Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

  42. 68:42

    يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍۢ وَيُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ

    Yawma yukshafu 'am saaqinw wa yud'awna ilas sujoodi falaa yastatee'oon

    Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.

  43. 68:43

    خَٰشِعَةً أَبْصَٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۖ وَقَدْ كَانُوا۟ يُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمْ سَٰلِمُونَ

    Khaashi'atan absaaruhum tarhaquhum zillatunw wa qad kaanoo yud'awna ilassujoodi wa hum saalimoon

    Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

  44. 68:44

    فَذَرْنِى وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ

    Fazarnee wa many yukazzibu bihaazal hadeesi sanastad rijuhum min haisu laa ya'lamoon

    Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

  45. 68:45

    وَأُمْلِى لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِى مَتِينٌ

    Wa umlee lahum; inna kaidee mateen

    Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.

  46. 68:46

    أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًۭا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍۢ مُّثْقَلُونَ

    Am tas'aluhum ajran fahum mim maghramim musqaloon

    Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

  47. 68:47

    أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ

    Am 'indahumul ghaibu fahum yaktuboon

    Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

  48. 68:48

    فَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌۭ

    Fasbir lihkmi rabbika wa laa takun kasaahibil boot; iz naadaa wa huwa makzoom

    Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

  49. 68:49

    لَّوْلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعْمَةٌۭ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ مَذْمُومٌۭ

    Law laaa an tadaara kahoo ni'matum mir rabbihee lanubiza bil'araaa'i wa huwa mazmoom

    Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

  50. 68:50

    فَٱجْتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

    Fajtabaahu rabbuhoo faja'alahoo minas saaliheen

    Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

  51. 68:51

    وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَٰرِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا۟ ٱلذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجْنُونٌۭ

    Wa iny-yakaadul lazeena kafaroo la-yuzliqoonaka biabsaarihim lammaa saml'uz-Zikra wa yaqooloona innahoo lamajnoon

    Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"

  52. 68:52

    وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَٰلَمِينَ

    Wa maa huwa illaa zikrul lil'aalameen

    Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.

About Surah Al-Qalam

Al-Qalam, the Pen, opens with an oath by the pen and what is written, and defends the Prophet (peace be upon him) against the insult that he was mad, affirming instead that he was of the highest character. It tells the parable of the owners of a garden who were humbled, and calls for patience and steadfastness.

Themes: The pen and writing, The Prophet's character, The owners of the garden, Patience

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.