All Surahs

Surah Al-Haqqah (undefined)

سُورَةُ الحَاقَّةِ

Surah 69 of the Holy Quran · Meccan · 52 verses

Also spelled: Haqqah, Al Haqqah, AlHaqqah, The Reality

Surah Al-Haqqah (undefined) is the 69th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 52 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 69:1

    ٱلْحَآقَّةُ

    Al haaaqqah

    Kiran gaskiya!

  2. 69:2

    مَا ٱلْحَآقَّةُ

    Mal haaaqqah

    Mẽne ne kiran gaskiya?

  3. 69:3

    وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ

    Wa maaa adraaka mal haaaqqah

    Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

  4. 69:4

    كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ

    Kazzabat samoodu wa 'Aadum bil qaari'ah

    Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

  5. 69:5

    فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ

    Fa-ammaa Samoodu fauhlikoo bittaaghiyah

    To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

  6. 69:6

    وَأَمَّا عَادٌۭ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍۢ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍۢ

    Wa ammaa 'Aadun fa uhlikoo bireehin sarsarin 'aatiyah

    Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

  7. 69:7

    سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍۢ وَثَمَٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًۭا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍۢ

    Sakhkharahaa 'alaihim sab'a la yaalinw wa samaaniyata ayyaamin husooman fataral qawma feehaa sar'aa ka annahum a'jaazu nakhlin khaawiyah

    (Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

  8. 69:8

    فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍۢ

    Fahal taraa lahum mim baaqiyah

    To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

  9. 69:9

    وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ

    Wa jaaa'a Firawnu wa man qablahoo wal mu'tafikaatu bilhaati'ah

    Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

  10. 69:10

    فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةًۭ رَّابِيَةً

    Fa'ansaw Rasoola Rabbihim fa akhazahum akhzatar raabiyah

    Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

  11. 69:11

    إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ

    Innaa lammaa taghal maaa'u hamalnaakum fil jaariyah

    Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

  12. 69:12

    لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةًۭ وَتَعِيَهَآ أُذُنٌۭ وَٰعِيَةٌۭ

    Linaj'alahaa lakum tazki ratanw-wa ta'iyahaa unzununw waa'iyah

    Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

  13. 69:13

    فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ

    Fa izaa nufikha fis soori nafkhatunw waahidah

    To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

  14. 69:14

    وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةًۭ وَٰحِدَةًۭ

    Wa humilatil ardu wal jibaalu fadukkataa dakkatanw waahidah

    Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

  15. 69:15

    فَيَوْمَئِذٍۢ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ

    Fa yawma'izinw waqa'atil waaqi'ah

    A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

  16. 69:16

    وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍۢ وَاهِيَةٌۭ

    Wanshaqqatis samaaa'u fahiya yawma 'izinw-waahiyah

    Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

  17. 69:17

    وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍۢ ثَمَٰنِيَةٌۭ

    Wal malaku 'alaaa arjaaa'ihaa; wa yahmilu 'Arsha Rabbika fawqahum yawma'izin samaaniyah

    Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

  18. 69:18

    يَوْمَئِذٍۢ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌۭ

    Yawma'izin tu'radoona laa takhfaa min kum khaafiyah

    A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

  19. 69:19

    فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَٰبِيَهْ

    Fa ammaa man ootiya kitaabahoo biyameenihee fa yaqoolu haaa'umuq ra'oo kitaabiyah

    To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

  20. 69:20

    إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَٰقٍ حِسَابِيَهْ

    Innee zannantu annee mulaaqin hisaabiyah

    "Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

  21. 69:21

    فَهُوَ فِى عِيشَةٍۢ رَّاضِيَةٍۢ

    Fahuwa fee 'eeshatir raadiyah

    Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

  22. 69:22

    فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ

    Fee jannnatin 'aaliyah

    A cikin Aljanna maɗaukakiya.

  23. 69:23

    قُطُوفُهَا دَانِيَةٌۭ

    Qutoofuhaa daaniyah

    Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

  24. 69:24

    كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ

    Kuloo washraboo haneee'am bimaaa aslaftum fil ayyaamil khaliyah

    (Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

  25. 69:25

    وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَٰبِيَهْ

    Wa ammaa man ootiya kitaabahoo bishimaalihee fa yaqoolu yaalaitanee lam oota kitaaabiyah

    Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

  26. 69:26

    وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ

    Wa lam adri maa hisaabiyah

    "Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

  27. 69:27

    يَٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ

    Yaa laitahaa kaanatil qaadiyah

    "In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

  28. 69:28

    مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ

    Maaa aghnaa 'annee maaliyah

    "Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

  29. 69:29

    هَلَكَ عَنِّى سُلْطَٰنِيَهْ

    Halaka 'annee sultaaniyah

    "Ĩkona ya ɓace mini!"

  30. 69:30

    خُذُوهُ فَغُلُّوهُ

    Khuzoohu faghullooh

    (Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

  31. 69:31

    ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ

    Summal Jaheema sallooh

    "Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

  32. 69:32

    ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍۢ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًۭا فَٱسْلُكُوهُ

    Summa fee silsilatin zar'uhaa sab'oona ziraa'an faslukooh

    "Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

  33. 69:33

    إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ

    Innahoo kaana laa yu'minubillaahil 'Azeem

    "Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

  34. 69:34

    وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ

    wa laa yahuddu 'alaa ta'aamil miskeen

    "Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

  35. 69:35

    فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَٰهُنَا حَمِيمٌۭ

    Falaysa lahul yawma haahunaa hameem

    "Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

  36. 69:36

    وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍۢ

    Wa laa ta'aamun illaa min ghisleen

    "Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

  37. 69:37

    لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَٰطِـُٔونَ

    Laa yaakuluhooo illal khati'oon

    "Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

  38. 69:38

    فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ

    Falaaa uqsimu bimaa tubsiroon

    To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

  39. 69:39

    وَمَا لَا تُبْصِرُونَ

    Wa maa laa tubsiroon

    Da abin da bã ku iya gani.

  40. 69:40

    إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ

    Innahoo laqawlu Rasoolin kareem

    Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

  41. 69:41

    وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تُؤْمِنُونَ

    Wa ma huwa biqawli shaa'ir; qaleelam maa tu'minoon

    Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

  42. 69:42

    وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تَذَكَّرُونَ

    Wa laa biqawli kaahin; qaleelam maa tazakkaroon

    Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

  43. 69:43

    تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

    Tanzeelum mir rabbil 'aalameen

    Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

  44. 69:44

    وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ

    Wa law taqawwala 'alainaa ba'dal aqaaweel

    Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

  45. 69:45

    لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ

    La-akhaznaa minhu bilyameen

    Dã Mun kãma shi da dãma.

  46. 69:46

    ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ

    Summa laqata'naa minhul wateen

    sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

  47. 69:47

    فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَٰجِزِينَ

    Famaa minkum min ahadin'anhu haajizeen

    Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

  48. 69:48

    وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌۭ لِّلْمُتَّقِينَ

    Wa innahoo latazkiratul lilmuttaqeen

    Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

  49. 69:49

    وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

    Wa inna lana'lamu anna minkum mukazzibeen

    Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

  50. 69:50

    وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَٰفِرِينَ

    Wa innahu lahasratun 'alal kaafireen

    Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

  51. 69:51

    وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ

    Wa innahoo lahaqqul yaqeen

    Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

  52. 69:52

    فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

    Fasbbih bismi Rabbikal 'Azeem

    Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.

About Surah Al-Haqqah

Al-Haqqah, the Reality, is a vivid surah about the certain Hour. It recalls the nations of 'Ad and Thamud, then describes the Day when the trumpet is blown and deeds are weighed, with the one given his record in his right hand rejoicing and the one given it in his left filled with regret. It affirms that the Quran is true revelation.

Themes: The certain Hour, Past nations, The record of deeds, Truth of revelation

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.