All Surahs

Surah As-Saffat (undefined)

سُورَةُ الصَّافَّاتِ

Surah 37 of the Holy Quran · Meccan · 182 verses

Also spelled: Saffat, As Saffat, AsSaffat, Those who set the Ranks

Surah As-Saffat (undefined) is the 37th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 182 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.

  1. 37:1

    وَٱلصَّٰٓفَّٰتِ صَفًّۭا

    Wassaaaffaati saffaa

    Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

  2. 37:2

    فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًۭا

    Fazzaajiraati zajraa

    Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.

  3. 37:3

    فَٱلتَّٰلِيَٰتِ ذِكْرًا

    Fattaaliyaati Zikra

    Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

  4. 37:4

    إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌۭ

    Inna Illaahakum la Waahid

    Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

  5. 37:5

    رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَٰرِقِ

    Rabbus samaawaati wal ardi wa maa bainahumaa wa Rabbul mashaariq

    Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

  6. 37:6

    إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ

    Innaa zaiyannas samaaa 'ad dunyaa bizeenatinil kawaakib

    Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

  7. 37:7

    وَحِفْظًۭا مِّن كُلِّ شَيْطَٰنٍۢ مَّارِدٍۢ

    Wa hifzam min kulli Shaitaanim maarid

    Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

  8. 37:8

    لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍۢ

    Laa yassamma 'oona ilal mala il a'alaa wa yuqzafoona min kulli jaanib

    Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

  9. 37:9

    دُحُورًۭا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌۭ وَاصِبٌ

    Duhooranw wa lahum 'azaabunw waasib

    Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

  10. 37:10

    إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌۭ ثَاقِبٌۭ

    Illaa man khatifal khatfata fa atba'ahoo shihaabun saaqib

    Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

  11. 37:11

    فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ ۚ إِنَّا خَلَقْنَٰهُم مِّن طِينٍۢ لَّازِبٍۭ

    Fastaftihim ahum ashaddu khalqan am man khalaqnaa; innaa khalaqnaahum min teenil laazib

    Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

  12. 37:12

    بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ

    Bal'ajibta wa yaskharoon

    Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

  13. 37:13

    وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ

    Wa izaa zukkiroo laa yazkuroon

    Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

  14. 37:14

    وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةًۭ يَسْتَسْخِرُونَ

    Wa izaa ra aw Aayatinw yastaskhiroon

    Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

  15. 37:15

    وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ مُّبِينٌ

    Wa qaalooo in haazaa illaa sihrum mubeen

    Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

  16. 37:16

    أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ

    'A-izaa mitnaa wa kunnaa turaabanw wa 'izaaman 'ainnaa lamab'oosoon

    "Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

  17. 37:17

    أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ

    Awa aabaa'unal awwaloon

    "Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

  18. 37:18

    قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ

    Qul na'am wa antum daakhiroon

    Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

  19. 37:19

    فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ

    Fa innamaa hiya zajra tunw waahidatun fa izaa hum yanzuroon

    Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

  20. 37:20

    وَقَالُوا۟ يَٰوَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ

    Qa qaaloo yaa wailanaa haazaa Yawmud-Deen

    Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

  21. 37:21

    هَٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

    Haazaa Yawmul Faslil lazee kuntum bihee tukaziboon

    Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

  22. 37:22

    ۞ ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ

    Uhshurul lazeena zalamoo wa azwaajahum wa maa kaanoo ya'budoon

    Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

  23. 37:23

    مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ

    Min doonil laahi fahdoohum ilaa siraatil Jaheem

    Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

  24. 37:24

    وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ

    Wa qifoohum innahum mas'ooloon

    Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

  25. 37:25

    مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ

    Maa lakum laa tanaasaroon

    Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

  26. 37:26

    بَلْ هُمُ ٱلْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ

    Bal humul Yawma mustaslimoon

    Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

  27. 37:27

    وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

    Wa aqbala ba'duhum 'alaa ba'diny yatasaaa'aloon

    Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

  28. 37:28

    قَالُوٓا۟ إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ ٱلْيَمِينِ

    Qaalooo innakum kuntum taatoonanaa 'anil yameen

    Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

  29. 37:29

    قَالُوا۟ بَل لَّمْ تَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ

    Qaaloo bal lam takoonoo mu'mineen

    Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

  30. 37:30

    وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَٰنٍۭ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًۭا طَٰغِينَ

    Wa maa kaana lanaa 'alaikum min sultaanim bal kuntum qawman taagheen

    "Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

  31. 37:31

    فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَآ ۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ

    Fahaqqa 'alainaa qawlu Rabbinaaa innaa lazaaa'iqoon

    "Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

  32. 37:32

    فَأَغْوَيْنَٰكُمْ إِنَّا كُنَّا غَٰوِينَ

    Fa aghwainaakum innaa kunnaa ghaaween

    "Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

  33. 37:33

    فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍۢ فِى ٱلْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ

    Fa innahum Yawma'izin fil'azaabi mushtarikoon

    To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

  34. 37:34

    إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ

    Innaa kazaalika naf'alu bil mujrimeen

    Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

  35. 37:35

    إِنَّهُمْ كَانُوٓا۟ إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ

    Innahum kaanooo izaa qeela lahum laaa ilaaha illal laahu yastakbiroon

    Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

  36. 37:36

    وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓا۟ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٍۢ مَّجْنُونٍۭ

    Wa yaqooloona a'innaa lataarikooo aalihatinaa lishaa'irim majnoon

    Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

  37. 37:37

    بَلْ جَآءَ بِٱلْحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلْمُرْسَلِينَ

    bal jaaa'a bilhaqqi wa saddaqal mursaleen

    Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

  38. 37:38

    إِنَّكُمْ لَذَآئِقُوا۟ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَلِيمِ

    Innakum lazaaa'iqul 'azaabil aleem

    Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

  39. 37:39

    وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

    Wa maa tujzawna illaa maa kuntum ta'maloon

    Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

  40. 37:40

    إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

    Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

    Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

  41. 37:41

    أُو۟لَٰٓئِكَ لَهُمْ رِزْقٌۭ مَّعْلُومٌۭ

    Ulaaa'ika lahum rizqum ma'loom

    Waɗannan sunã da abinci sananne.

  42. 37:42

    فَوَٰكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ

    Fa waakihu wa hum mukramoon

    'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

  43. 37:43

    فِى جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

    Fee jannaatin Na'eem

    A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

  44. 37:44

    عَلَىٰ سُرُرٍۢ مُّتَقَٰبِلِينَ

    'Alaa sururim mutaqaa bileen

    A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

  45. 37:45

    يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍۢ مِّن مَّعِينٍۭ

    Yutaafu 'alaihim bikaasim mim ma'een

    Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

  46. 37:46

    بَيْضَآءَ لَذَّةٍۢ لِّلشَّٰرِبِينَ

    Baidaaa'a laz zatil lish shaaribeen

    Farã mai dãɗi ga mashãyan.

  47. 37:47

    لَا فِيهَا غَوْلٌۭ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ

    Laa feehaa ghawlunw wa laa hum 'anhaa yunzafoon

    A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

  48. 37:48

    وَعِندَهُمْ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ عِينٌۭ

    Wa 'indahum qaasiraatut tarfi 'een

    Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

  49. 37:49

    كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌۭ مَّكْنُونٌۭ

    Ka annahunna baidum maknoon

    Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

  50. 37:50

    فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

    Fa aqbala ba'duhum 'alaa badiny yatasaaa 'aloon

    Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

  51. 37:51

    قَالَ قَآئِلٌۭ مِّنْهُمْ إِنِّى كَانَ لِى قَرِينٌۭ

    Qaala qaaa'ilum minhum innee kaana lee qareen

    Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

  52. 37:52

    يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلْمُصَدِّقِينَ

    Yaqoolu a'innnaka laminal musaddiqeen

    Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

  53. 37:53

    أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ

    'A-izaa mitnaa wa kunnaa turaabanw wa 'izaaman 'ainnaa lamadeenoon

    "Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

  54. 37:54

    قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ

    Qaala hal antum muttali'oon

    (Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

  55. 37:55

    فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِى سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ

    Fattala'a fara aahu fee sawaaa'il Jaheem

    Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

  56. 37:56

    قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ

    Qaala tallaahi in kitta laturdeen

    Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

  57. 37:57

    وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّى لَكُنتُ مِنَ ٱلْمُحْضَرِينَ

    Wa law laa ni'matu Rabbee lakuntu minal muhdareen

    "Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

  58. 37:58

    أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ

    Afamaa nahnu bimaiyiteen

    "Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

  59. 37:59

    إِلَّا مَوْتَتَنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ

    Illa mawtatanal oola wa maa nahnu bimu'azzabeen

    "Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

  60. 37:60

    إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ

    Inna haazaa falya'ma lil'aamiloon

    Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

  61. 37:61

    لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ ٱلْعَٰمِلُونَ

    Limisli haaza falya'ma lil 'aamiloon

    Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

  62. 37:62

    أَذَٰلِكَ خَيْرٌۭ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ

    Azaalika khairun nuzulan am shajaratuz Zaqqom

    Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

  63. 37:63

    إِنَّا جَعَلْنَٰهَا فِتْنَةًۭ لِّلظَّٰلِمِينَ

    Innaa ja'alnaahaa fitnatal lizzaalimeen

    Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

  64. 37:64

    إِنَّهَا شَجَرَةٌۭ تَخْرُجُ فِىٓ أَصْلِ ٱلْجَحِيمِ

    Innahaa shajaratun takhruju feee aslil Jaheem

    Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

  65. 37:65

    طَلْعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ

    Tal'uhaa ka annahoo ru'oosush Shayaateen

    Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

  66. 37:66

    فَإِنَّهُمْ لَءَاكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ

    Fa innahum la aakiloona minhaa famaali'oona minhal butoon

    To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

  67. 37:67

    ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًۭا مِّنْ حَمِيمٍۢ

    Summa inna lahum 'alaihaa lashawbam min hameem

    Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

  68. 37:68

    ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى ٱلْجَحِيمِ

    Summa inna marji'ahum la ilal Jaheem

    Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

  69. 37:69

    إِنَّهُمْ أَلْفَوْا۟ ءَابَآءَهُمْ ضَآلِّينَ

    Innahum alfaw aabaaa'ahum daaalleen

    Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

  70. 37:70

    فَهُمْ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمْ يُهْرَعُونَ

    Fahum 'alaa aasaarihim yuhra'oon

    Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

  71. 37:71

    وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ ٱلْأَوَّلِينَ

    Wa laqad dalla qablahum aksarul awwaleen

    Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

  72. 37:72

    وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

    Wa laqad arsalnaa feehim munzireen

    Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

  73. 37:73

    فَٱنظُرْ كَيْفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلْمُنذَرِينَ

    Fanzur kaifa kaana 'aaqibatul munzareen

    Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

  74. 37:74

    إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

    Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

    Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

  75. 37:75

    وَلَقَدْ نَادَىٰنَا نُوحٌۭ فَلَنِعْمَ ٱلْمُجِيبُونَ

    Wa laqad naadaanaa Noohun falani'mal mujeeboon

    Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

  76. 37:76

    وَنَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥ مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

    Wa jajainaahu wa ahlahoo minal karbil 'azeem

    Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

  77. 37:77

    وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلْبَاقِينَ

    Wa ja'alnaa zurriyyatahoo hummul baaqeen

    Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

  78. 37:78

    وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

    Wa taraknaa 'alaihi fil aakhireen

    Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

  79. 37:79

    سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٍۢ فِى ٱلْعَٰلَمِينَ

    Salaamun 'alaa Noohin fil 'aalameen

    Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

  80. 37:80

    إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

    Innaa kazaalika najzil muhsineen

    Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

  81. 37:81

    إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

    Innahoo min 'ibaadinal mu'mineen

    Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.

  82. 37:82

    ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْءَاخَرِينَ

    Summa aghraqnal aakhareen

    Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

  83. 37:83

    ۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبْرَٰهِيمَ

    Wa ina min shee'atihee la Ibraaheem

    Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

  84. 37:84

    إِذْ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلْبٍۢ سَلِيمٍ

    Iz jaaa'a Rabbahoo bi qalbin saleem

    A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

  85. 37:85

    إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَاذَا تَعْبُدُونَ

    Iz qaala li abeehi wa qawmihee maazaa ta'budoon

    A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

  86. 37:86

    أَئِفْكًا ءَالِهَةًۭ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ

    A'ifkan aalihatan doonal laahi tureedoon

    "Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

  87. 37:87

    فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

    Famaa zannukum bi Rabbil'aalameen

    "To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

  88. 37:88

    فَنَظَرَ نَظْرَةًۭ فِى ٱلنُّجُومِ

    Fanazara nazratan finnujoom

    Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

  89. 37:89

    فَقَالَ إِنِّى سَقِيمٌۭ

    Faqaala inee saqeem

    Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

  90. 37:90

    فَتَوَلَّوْا۟ عَنْهُ مُدْبِرِينَ

    Fatawallaw 'anhu mudbireen

    Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

  91. 37:91

    فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ

    Faraagha ilaaa aalihatihim faqaala alaa taakuloon

    Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

  92. 37:92

    مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ

    Maa lakum laa tantiqoon

    "Me ya sãme ku, bã ku magana?"

  93. 37:93

    فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًۢا بِٱلْيَمِينِ

    Faraagha 'alaihim darbam bilyameen

    Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

  94. 37:94

    فَأَقْبَلُوٓا۟ إِلَيْهِ يَزِفُّونَ

    Fa aqbalooo ilaihi yaziffoon

    Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

  95. 37:95

    قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ

    Qaala ata'budoona maa tanhitoon

    Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

  96. 37:96

    وَٱللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ

    Wallaahu khalaqakum wa maa ta'maloon

    "Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

  97. 37:97

    قَالُوا۟ ٱبْنُوا۟ لَهُۥ بُنْيَٰنًۭا فَأَلْقُوهُ فِى ٱلْجَحِيمِ

    Qaalub noo lahoo bun yaanan fa alqoohu fil jaheem

    Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

  98. 37:98

    فَأَرَادُوا۟ بِهِۦ كَيْدًۭا فَجَعَلْنَٰهُمُ ٱلْأَسْفَلِينَ

    Fa araadoo bihee kaidan faja 'alnaahumul asfaleen

    Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

  99. 37:99

    وَقَالَ إِنِّى ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّى سَيَهْدِينِ

    Wa qaala innee zaahibun ilaa Rabbee sa yahdeen

    Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

  100. 37:100

    رَبِّ هَبْ لِى مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

    Rabbi hab lee minas saaliheen

    "Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

  101. 37:101

    فَبَشَّرْنَٰهُ بِغُلَٰمٍ حَلِيمٍۢ

    Fabashsharnaahu bighulaamin haleem

    Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.

  102. 37:102

    فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعْىَ قَالَ يَٰبُنَىَّ إِنِّىٓ أَرَىٰ فِى ٱلْمَنَامِ أَنِّىٓ أَذْبَحُكَ فَٱنظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَٰٓأَبَتِ ٱفْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِىٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّٰبِرِينَ

    Falamma balagha ma'a hus sa'ya qaala yaa buniya inneee araa fil manaami anneee azbahuka fanzur maazaa taraa; qaala yaaa abatif 'al maa tu'maru satajidunee in shaaa'allaahu minas saabireen

    To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

  103. 37:103

    فَلَمَّآ أَسْلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلْجَبِينِ

    Falammaaa aslamaa wa tallahoo liljabeen

    To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.

  104. 37:104

    وَنَٰدَيْنَٰهُ أَن يَٰٓإِبْرَٰهِيمُ

    Wa naadainaahu ai yaaaa Ibraheem

    Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

  105. 37:105

    قَدْ صَدَّقْتَ ٱلرُّءْيَآ ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

    Qad saddaqtar ru'yaa; innaa kazaalika najzil muhsineen

    "Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

  106. 37:106

    إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلْبَلَٰٓؤُا۟ ٱلْمُبِينُ

    Inna haazaa lahuwal balaaa'ul mubeen

    Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

  107. 37:107

    وَفَدَيْنَٰهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍۢ

    Wa fadainaahu bizibhin 'azeem

    Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

  108. 37:108

    وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

    Wa taraknaa 'alaihi fil aakhireen

    Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

  109. 37:109

    سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِبْرَٰهِيمَ

    Salaamun 'alaaa Ibraaheem

    Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

  110. 37:110

    كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

    Kazaalika najzil muhsineen

    Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

  111. 37:111

    إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

    Innahoo min 'ibaadinal mu'mineen

    Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

  112. 37:112

    وَبَشَّرْنَٰهُ بِإِسْحَٰقَ نَبِيًّۭا مِّنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

    Wa bashsharnaahu bi Ishaaqa Nabiyayam minas saaliheen

    Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

  113. 37:113

    وَبَٰرَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰٓ إِسْحَٰقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌۭ وَظَالِمٌۭ لِّنَفْسِهِۦ مُبِينٌۭ

    Wa baaraknaa 'alaihi wa 'alaaa Ishaaq; wa min zurriyya tihimaa muhsinunw wa zaalimul linafshihee mubeen

    Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

  114. 37:114

    وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

    Wa laqad mananna alaa Moosaa wa Haaroon

    Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

  115. 37:115

    وَنَجَّيْنَٰهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

    Wa najjainaahumaa wa qawmahumaa minal karbil 'azeem

    Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

  116. 37:116

    وَنَصَرْنَٰهُمْ فَكَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَٰلِبِينَ

    Wa nasarnaahum fakaanoo humul ghaalibeen

    Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

  117. 37:117

    وَءَاتَيْنَٰهُمَا ٱلْكِتَٰبَ ٱلْمُسْتَبِينَ

    Wa aatainaahumal Kitaabal mustabeen

    Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

  118. 37:118

    وَهَدَيْنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ

    Wa hadainaahumus Siraatal Mustaqeem

    Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

  119. 37:119

    وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِى ٱلْءَاخِرِينَ

    Wa taraknaa 'alaihimaa fil aakhireen

    Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

  120. 37:120

    سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

    Salaamun 'alaa Moosaa wa Haaroon

    Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

  121. 37:121

    إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

    Innaa kazaalika najzil muhsineen

    Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

  122. 37:122

    إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

    Innahumaa min 'ibaadinal mu'mineen

    Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.

  123. 37:123

    وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

    Wa inna Ilyaasa laminal mursaleen

    Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

  124. 37:124

    إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ

    Iz qaala liqawmiheee alaa tattaqoon

    A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

  125. 37:125

    أَتَدْعُونَ بَعْلًۭا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ ٱلْخَٰلِقِينَ

    Atad'oona Ba'lanw wa tazaroona ahsanal khaaliqeen

    "Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

  126. 37:126

    ٱللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ

    Allaaha Rabbakum wa Rabba aabaaa'ikumul awwaleen

    "Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"

  127. 37:127

    فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

    Fakazzaboohu fa inna hum lamuhdaroon

    Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

  128. 37:128

    إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

    Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

    Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

  129. 37:129

    وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

    Wa taraknaa 'alaihi fil aakhireen

    Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

  130. 37:130

    سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلْ يَاسِينَ

    Salaamun 'alaaa Ilyaaseen

    Aminci ya tabbata ga Ilyãs.

  131. 37:131

    إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

    Innaa kazaalika najzil muhsineen

    Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

  132. 37:132

    إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

    Innahoo min 'ibaadinal mu'mineen

    Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

  133. 37:133

    وَإِنَّ لُوطًۭا لَّمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

    Wa inna Lootal laminal mursaleen

    Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

  134. 37:134

    إِذْ نَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

    Iz najjainaahu wa ahlahooo ajma'een

    A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

  135. 37:135

    إِلَّا عَجُوزًۭا فِى ٱلْغَٰبِرِينَ

    Illaa 'ajoozan fil ghaabireen

    Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

  136. 37:136

    ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْءَاخَرِينَ

    Summa dammarnal aakhareen

    Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

  137. 37:137

    وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ

    Wa innakum latamurroona 'alaihim musbiheen

    Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

  138. 37:138

    وَبِٱلَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ

    Wa billail; afalaa ta'qiloon

    Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

  139. 37:139

    وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

    Wa inna Yoonusa laminal mursaleen

    Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

  140. 37:140

    إِذْ أَبَقَ إِلَى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ

    Iz abaqa ilal fulkil mash hoon

    A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

  141. 37:141

    فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلْمُدْحَضِينَ

    Fasaahama fakaana minal mudhadeen

    Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

  142. 37:142

    فَٱلْتَقَمَهُ ٱلْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌۭ

    Faltaqamahul hootu wa huwa muleem

    Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

  143. 37:143

    فَلَوْلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلْمُسَبِّحِينَ

    Falaw laaa annahoo kaana minal musabbiheen

    To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

  144. 37:144

    لَلَبِثَ فِى بَطْنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ

    Lalabisa fee batniheee ilaa Yawmi yub'asoon

    Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

  145. 37:145

    ۞ فَنَبَذْنَٰهُ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٌۭ

    Fanabaznaahu bil'araaa'i wa huwa saqeem

    Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

  146. 37:146

    وَأَنۢبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةًۭ مِّن يَقْطِينٍۢ

    Wa ambatnaa 'alaihi shajaratam mai yaqteen

    Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

  147. 37:147

    وَأَرْسَلْنَٰهُ إِلَىٰ مِا۟ئَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ

    Wa arsalnaahu ilaa mi'ati alfin aw yazeedoon

    Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

  148. 37:148

    فَـَٔامَنُوا۟ فَمَتَّعْنَٰهُمْ إِلَىٰ حِينٍۢ

    Fa aamanoo famatta' naahum ilaa heen

    Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

  149. 37:149

    فَٱسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ ٱلْبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلْبَنُونَ

    Fastaftihim ali Rabbikal banaatu wa lahumul banoon

    Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

  150. 37:150

    أَمْ خَلَقْنَا ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ إِنَٰثًۭا وَهُمْ شَٰهِدُونَ

    Am khalaqnal malaaa'i kata inaasanw wa hm shaahidoon

    Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

  151. 37:151

    أَلَآ إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ

    Alaaa innahum min ifkihim la yaqooloon

    To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

  152. 37:152

    وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَٰذِبُونَ

    Waladal laahu wa innhum lakaaziboon

    "Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

  153. 37:153

    أَصْطَفَى ٱلْبَنَاتِ عَلَى ٱلْبَنِينَ

    Astafal banaati 'alal baneen

    Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

  154. 37:154

    مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

    Maa lakum kaifa tahkumoon

    Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?

  155. 37:155

    أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

    Afalaa tazakkaroon

    Shin, bã ku tunãni?

  156. 37:156

    أَمْ لَكُمْ سُلْطَٰنٌۭ مُّبِينٌۭ

    Am lakum sultaanum mubeen

    Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

  157. 37:157

    فَأْتُوا۟ بِكِتَٰبِكُمْ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ

    Faatoo bi Kitaabikum in kuntum saadiqeen

    To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

  158. 37:158

    وَجَعَلُوا۟ بَيْنَهُۥ وَبَيْنَ ٱلْجِنَّةِ نَسَبًۭا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ ٱلْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

    Wa ja'aloo bainahoo wa bainal jinnati nasabaa; wa laqad 'alimatil jinnatu innahum lamuhdaroon

    Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

  159. 37:159

    سُبْحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

    Subhaanal laahi 'ammaa yasifoon

    Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

  160. 37:160

    إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

    Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

    Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

  161. 37:161

    فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ

    Fa innakum wa maa ta'ubdoon

    To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

  162. 37:162

    مَآ أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَٰتِنِينَ

    Maaa antum 'alaihi befaaatineen

    Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

  163. 37:163

    إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ ٱلْجَحِيمِ

    Illaa man huwa saalil jaheem

    Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

  164. 37:164

    وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٌۭ مَّعْلُومٌۭ

    Wa maa minnasa illaa lahoo maqaamum ma'loom

    "Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."

  165. 37:165

    وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلصَّآفُّونَ

    Wa innaa llanah nus saaffoon

    "Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

  166. 37:166

    وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلْمُسَبِّحُونَ

    Wa innaa lanah nul musabbihoon

    "Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

  167. 37:167

    وَإِن كَانُوا۟ لَيَقُولُونَ

    Wa in kaanoo la yaqooloon

    Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

  168. 37:168

    لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًۭا مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

    Law anna 'indana zikram minal awwaleen

    "Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

  169. 37:169

    لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

    Lakunna 'ibaadal laahil mukhlaseen

    "Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

  170. 37:170

    فَكَفَرُوا۟ بِهِۦ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ

    Fakafaroo bihee fasawfa ya'lamoon

    Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

  171. 37:171

    وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلْمُرْسَلِينَ

    Wa laqad sabaqat Kalimatunaa li'ibaadinal mursa leen

    Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

  172. 37:172

    إِنَّهُمْ لَهُمُ ٱلْمَنصُورُونَ

    Innaa hum lahumul mansooroon

    Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

  173. 37:173

    وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلْغَٰلِبُونَ

    Wa inna jundana lahumul ghaaliboon

    Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

  174. 37:174

    فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ

    Fatawalla 'anhum hatta heen

    Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

  175. 37:175

    وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

    Wa absirhum fasawfa yubsiroon

    Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.

  176. 37:176

    أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ

    Afabi'azaabinaa yasta'jiloon

    Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

  177. 37:177

    فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلْمُنذَرِينَ

    Fa izaa nazala bisaahatihim fasaaa'a sabaahul munzareen

    To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

  178. 37:178

    وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ

    Wa tawalla 'anhum hattaa heen

    Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

  179. 37:179

    وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

    Wa absir fasawfa yubsiroon

    Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

  180. 37:180

    سُبْحَٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ

    Subhaana Rabbika Rabbil 'izzati 'amma yasifoon

    Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

  181. 37:181

    وَسَلَٰمٌ عَلَى ٱلْمُرْسَلِينَ

    Wa salaamun 'alalmursaleen

    Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

  182. 37:182

    وَٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

    Walhamdu lillaahi Rabbil 'aalameen

    Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.

About Surah As-Saffat

As-Saffat, Those Who Set the Ranks, opens with the angels arrayed in rows in worship. It recounts the trials of several prophets, most movingly Ibrahim and his readiness to sacrifice his son, and the rescue that followed. It also recalls Nuh, Musa, Ilyas, Lut, and Yunus, drawing a line of devotion through all of them.

Themes: The angels in worship, Ibrahim's sacrifice, Lives of the prophets, Devotion

Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.