Surah Al-Mursalat (undefined) is the 77th chapter of the Holy Quran. It was revealed in Mecca and contains 50 verses (ayahs). Read it below with the Arabic text, transliteration, and Hausa translation, or open it as interactive flashcards to memorize it verse by verse.
- 77:1
وَٱلْمُرْسَلَٰتِ عُرْفًۭا
Wal mursalaati'urfaa
Ina rantsuwa da iskõkin da ake sakõwa jẽre, sunã bin jũna.
- 77:2
فَٱلْعَٰصِفَٰتِ عَصْفًۭا
Fal'aasifaati 'asfaa
Sa'an nan, su zamã iskõki mãsu ƙarfi suna kaɗãwa da ƙarfi.
- 77:3
وَٱلنَّٰشِرَٰتِ نَشْرًۭا
Wannaashiraati nashraa
Kuma, mãsu watsa rahama wãtsãwa.
- 77:4
فَٱلْفَٰرِقَٰتِ فَرْقًۭا
Falfaariqaati farqaa
sa'an nan, da ãyõyi mãsu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabẽwa.
- 77:5
فَٱلْمُلْقِيَٰتِ ذِكْرًا
Falmulqiyaati zikra
Sa'an nan da malã'iku mãsu jẽfa tunãtarwa ga Manzanni.
- 77:6
عُذْرًا أَوْ نُذْرًا
'Uzran aw nuzraa
Domin yanke hamzari ko dõmin gargadi.
- 77:7
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٌۭ
Innamaa too'adoona lawaaqi'
Lalle ne, abin da ake yi muku wa'adi da shi tabbas mai aukuwa ne
- 77:8
فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتْ
Fa izam nujoomu tumisat
To, idan taurãri aka shãfe haskensu.
- 77:9
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتْ
Wa izas samaaa'u furijat
Kuma, idan sama aka tsãge ta.
- 77:10
وَإِذَا ٱلْجِبَالُ نُسِفَتْ
Wa izal jibaalu nusifat
Kuma, idan duwãtsu aka nike su.
- 77:11
وَإِذَا ٱلرُّسُلُ أُقِّتَتْ
Wa izar Rusulu uqqitat
Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lõkacin tãra su.
- 77:12
لِأَىِّ يَوْمٍ أُجِّلَتْ
Li ayyi yawmin ujjilat
Domin babbar rãnar da aka yi wa ajali.
- 77:13
لِيَوْمِ ٱلْفَصْلِ
Li yawmil Fasl
Domin rãnar rarrabẽwa.
- 77:14
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ
Wa maaa adraaka maa yawmul fasl
Kuma, me ya sanar da kai rãnar rarrabẽwa?
- 77:15
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailuny yawma 'izillilmukazzibeen
Bone yã tabbata a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:16
أَلَمْ نُهْلِكِ ٱلْأَوَّلِينَ
Alam nuhlikil awwaleen
Ashe, ba Mu halakar da (mãsu ƙaryatãw) na farko ba.
- 77:17
ثُمَّ نُتْبِعُهُمُ ٱلْءَاخِرِينَ
Summa nutbi'uhumul aakhireen
Sa'an nan, kuma zã Mu biyar musu da na ƙarshe?
- 77:18
كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ
Kazzlika naf'alu bilmujrimeen
Haka nan, Muke aikatãwa da mãsu yin laifi.
- 77:19
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailunw yawma 'izil lil mukazzibeen
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:20
أَلَمْ نَخْلُقكُّم مِّن مَّآءٍۢ مَّهِينٍۢ
Alam nakhlukkum mimmaaa'im maheen
Ashe, ba Mu halitta ku daga wani ruwa wulakantacce ba.
- 77:21
فَجَعَلْنَٰهُ فِى قَرَارٍۢ مَّكِينٍ
Faja'alnaahu fee qaraarim makeen
Sa'an nan Muka sanya shi a cikin wani wurin natsuwa amintacce.
- 77:22
إِلَىٰ قَدَرٍۢ مَّعْلُومٍۢ
Illaa qadrim ma'loom
Zuwa ga wani gwargwadon mudda sananna.
- 77:23
فَقَدَرْنَا فَنِعْمَ ٱلْقَٰدِرُونَ
Faqadarnaa fani'mal qaadiroon
Sa'an nan, Muka nũna iyãwarMu? Madalla da Mu, Mãsu nũna iyãwa.
- 77:24
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailuny yawma 'izil lilmukazzibeen
Bone ya tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:25
أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ كِفَاتًا
Alam naj'alil arda kifaataa
Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattarã ba.
- 77:26
أَحْيَآءًۭ وَأَمْوَٰتًۭا
Ahyaaa'anw wa amwaataa
Ga rãyayyu da matattu,
- 77:27
وَجَعَلْنَا فِيهَا رَوَٰسِىَ شَٰمِخَٰتٍۢ وَأَسْقَيْنَٰكُم مَّآءًۭ فُرَاتًۭا
Wa ja'alnaa feehaa rawaasiya shaamikhaatinw wa asqainaakum maaa'an furaataa
Kuma, Muka sanya, a cikinta, kafaffun duwãtsu maɗaukaka, kuma Muka shayar da ku ruwa mai dãɗi?
- 77:28
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailuny yawma 'izil lilmukazzibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:29
ٱنطَلِقُوٓا۟ إِلَىٰ مَا كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
Intaliqooo ilaa maa kuntum bihee tukazziboon
Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi!
- 77:30
ٱنطَلِقُوٓا۟ إِلَىٰ ظِلٍّۢ ذِى ثَلَٰثِ شُعَبٍۢ
Intaliqooo ilaa zillin zee salaasi shu'ab
Ku tafi zuwa ga wata inuwa mai rassa uku.
- 77:31
لَّا ظَلِيلٍۢ وَلَا يُغْنِى مِنَ ٱللَّهَبِ
Laa zaleelinw wa laa yughnee minal lahab
Ita ba inuwar ba, kuma ba ta wadãtarwa daga harshen wuta.
- 77:32
إِنَّهَا تَرْمِى بِشَرَرٍۢ كَٱلْقَصْرِ
Innahaa tarmee bishararin kalqasr
Lalle ne, ita, tanã jifã da tartsatsi kamar sõraye.
- 77:33
كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٌۭ صُفْرٌۭ
Ka annahoo jimaalatun sufr
Kamar dai su raƙumma ne baƙãƙe.
- 77:34
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailuny yawma 'izil lilmukazibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:35
هَٰذَا يَوْمُ لَا يَنطِقُونَ
Haazaa yawmu laa uantiqoon
Wannan, yini ne da bã zã su iya yin magana ba.
- 77:36
وَلَا يُؤْذَنُ لَهُمْ فَيَعْتَذِرُونَ
Wa laa yu'zanu lahum fa ya'taziroon
Bã zã a yi musu izni ba, balle su kãwo hanzari.
- 77:37
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailunw yawma 'izil lilmukazzibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:38
هَٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ۖ جَمَعْنَٰكُمْ وَٱلْأَوَّلِينَ
Haaza yawmul fasli jama 'naakum wal awwaleen
Wannan rãnar rarrabẽwa ce, Mun tattara ku tare da mutãnen farko.
- 77:39
فَإِن كَانَ لَكُمْ كَيْدٌۭ فَكِيدُونِ
Fa in kaana lakum kaidun fakeedoon
To, idan akwai wata dabara gare ku, sai ku yi ma Ni ita.
- 77:40
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailuny yawma'izil lilmukazzibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:41
إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى ظِلَٰلٍۢ وَعُيُونٍۢ
Innal muttaqeena fee zilaalinw wa 'uyoon
Lalle ne, mãsu taƙawa suna a cikin inuwõwi da marẽmari.
- 77:42
وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشْتَهُونَ
Wa fawaakiha mimmaa yastahoon
Da wasu 'ya'yan itãce irin waɗanda suke marmari.
- 77:43
كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
Kuloo washraboo haneee 'am bimaa kuntum ta'maloon
(A ce musu) "Ku ci ku sha cikin ni'ima sabõda abin da kuka kasance kuna aikatãwa."
- 77:44
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
Innaa kazaalika najzil muhsineen
Lalle ne, Mũ haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
- 77:45
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailuny yawma 'izil lilmuzkazzibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:46
كُلُوا۟ وَتَمَتَّعُوا۟ قَلِيلًا إِنَّكُم مُّجْرِمُونَ
Kuloo wa tamatta'oo qaleelan innakum mujrimoon
(Ana ce musu) "Ku ci ku ji ɗan dãdi kaɗan, lalle ne dai ku mãsu laifi ne."
- 77:47
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailunny yawma 'izil lilmukazzibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:48
وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱرْكَعُوا۟ لَا يَرْكَعُونَ
Wa izaa qeela lahumur ka'oo aa yarka'oon
Kuma, idan an ce musu: "Ku yi rukũ'i; bã zã su yi rukũ'in (salla) ba."
- 77:49
وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Wailunny yawma 'izil lilmukazzibeen
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!
- 77:50
فَبِأَىِّ حَدِيثٍۭ بَعْدَهُۥ يُؤْمِنُونَ
Fabi ayyi hadeesim ba'dahoo yu'minoon
To, da wane lãbãri (Littãfi), waninsa (Alƙur'ãni) zã su yi ĩmãni
About Surah Al-Mursalat
Al-Mursalat, the Emissaries, opens with oaths by the winds sent forth and repeats a sobering refrain warning those who deny the truth. It points to the stages of human creation, the firm mountains, and the alternation of life as signs that the Day of Decision is real and certain.
Themes: Oaths and warning, Signs in creation, The Day of Decision, Accountability
Arabic: Uthmani script (Hafs). Translation: Hausa. Recitation: Mishary Rashid Alafasy. See Sources for full attribution.